Muhimman Abubuwa 4 da Jam'iyyun Adawa Suka Yi Matsaya gabanin Zaben 2027
Ibadan, Oyo State - A karshen makon da ya gabata ne 'yan adawar Najeriya suka gudanar da wani taro a birnin Ibadan na jihar Oyo a wani mataki na kulla hadaka gabanin 2027.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Wakilan jam'iyyun fiye da 10 sun halarci wannan taro, wanda suka shirya domin hada karfi da karfe da nufin kwace mulki daga hannun shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da jam'iyyarsa ta APC.

Source: Facebook
Jiga-jigan adawa sun hadu a Ibadan
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar na cikin manyan jiga-jigan da suka halarci wannan taro kamar yadda ya tabbatar a shafinsa na Facebook.
Tsofaffin yan takarar shugaban kasa, Rabiu Musa Kwankwaso da Peter Obi, tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, Gwamna Seyi Makinde, sanatoci da yan Majalisar tarayya na jam'iyyun adawa sun halarci wannan taro.
Jam'iyyun adawa da suka halarci taron
Haka nan kuma jam'iyyun adawa da suka halarci taron sun hada da ADC, PDP, LP, NNPP, PRP, Accord, APM, YP, ADP, da sauran makamantansu.
A taron dai manyam jam'iyyun adawa kamar ADC, NNPP da PDP sun nuna cewa abu ne mai wahala a iya kayar da Shugaba Tinubu matukar tsagin adawa ba su dunkule wuri guda ba.
Bisa haka ne yan adawar suka yi nazari tare da cimma matsaya kan muhimman batutuwa da suka shafi zaben 2027 wanda ke kara kusantowa.
Muhimman abubuwan da suka yi matsaya
Legit Hausa ta tattaro muku muhimman abubuwa hudu da jagororin adawar Najeriya suka cimma matsaya a wannan tafo domin tunkarar zaben 2027.
1. Tsaida dan takarar shugaban kasa 1
Yayin taron, manyan jam'iyyun adawa, PDP, LP, ADC da NNPP sun bada shawarar hada kai gaba daya domin tunkarar zaben 2027.
Vanguard ta ruwaito cewa sakamakon haka, jam'iyyun da suka halarci taron suka cimma matsayar cewa za su dunkule wuri guda, su fitar da dan takarar shugaban kasa guda daya, kuma su mara masa baya don ceto kasa.
2. Bukatar cire shugaban INEC
Wani abu da jam'iyyun adawar suka amince da shi, shi ne batun shugaban hukumar zabe mai zaman kanta da kasa (INEC), Farfesa Joash Amupitan.
'Yan adawar sun yanke shawarar cewa za su ci gaba da matsa wa gwamnati lamba da kiraye-kirayen sauya shugaban INEC domin a cewarsu, ta haka ne za a shirya sahihin zabe, kamar yadda Channels tv ta rahoto.
Tun bayan nada Farfesa Amuptan ya fara shan suka daga bangarori daban-daban ciki har da jam'iyyun adawa kamar ADC, inda suka bukaci ya yi murabus daga mukamin.

Source: Facebook
Jam'iyyun adawa sun zargi Amupitan da nuna son kai da goyon baya ga jam'iyyar APC mai mulki, shi yasa suke ganin bai kamata ya jagoranci shirya zaɓen gama-gari na 2027 ba.
3. Sake gyara dokar zaben Najeriya
Bugu da kari, 'yan adawar sun tattauna kan dokar zabe ta 2026 wacce Majalisar tarayya ta 10 ta yi wa garambawul a watannin da suka wuce.

Kara karanta wannan
Emefiele: An ji yadda aka yi amfani da sa hannun Buhari aka cire makudan kudi a bankin CBN
A taron da suka gudanar, hadakar jam'iyyun adawa sun amince cewa za su ci gaba da kiraye-kiraye domin Majalisar ta sake gyara wannan doka da suke ganin barazana ce ga zabe.
Sun ce ya zama dole Majalisa ta cire dukkan sassan da ke barazana ga sahihancin zaɓe, kuma waɗanda suka saɓa da tanade-tanaden kundin tsarin mulki, in ji rahoton BBC Hausa.
4. Gyara jadawalin zaben 2027
Haka zalika, jam'iyyun adawa zama da 10 da suka halarci wannan taro sun nuna damuwarsa kan wasu kayyadaddun lokuta da gindaya a jadawalin zaben 2027 musammn wa'adin tsaida yan takara.
Sun bayyana cewa sun dauki ƙa'idojin da INEC ta fitar a jadawalin a matsayin cikas, waɗanda aka tsara da gangan domin ƙaƙaba wa jam'iyyun adawa sharudda da wa'adin lokaci.
Don haka suka jaddada cewa suna buƙatar INEC ta tsawaita wa'adin gudanar da zaɓen fitar da gwani har zuwa ƙarshen watan Yuli, 2026, kamar yadda Tribune Online ta kawo.

Source: Facebook
INEC ta maida sunayen shugabannin ADC
A wani rahoton, kun ji cewa hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta sabunta bayanan shafinta na yanar gizo, biyo bayan hukuncin Kotun Koli kan shugabancin jam'iyyar ADC.
Hukumar INEC ta maida sunayen Sanata David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC na kasa da Rauf Aregbesola a matsayin sakataren jam'iyyar hadaka.
Wannan ci gaba ya soke matakin da INEC ta ɗauka a farkon watan Afrilu na cire shugabancin da Mark ke jagoranta daga shafinta, inda ta dogara da hukuncin kotun ɗaukaka ƙara.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


