Hankali Ya Kwanta, Kotun Kolin Najeriya Ta Yanke Hukunci kan Rikicin Jam'iyyar ADC

Hankali Ya Kwanta, Kotun Kolin Najeriya Ta Yanke Hukunci kan Rikicin Jam'iyyar ADC

Abuja, Nigeria - Kotun Kolin Najeriya ta yanke hukunci a karar da shigar gabanta game da rikicin shugabanci da ya addabi jam'iyyar yan hamayya ta ADC.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Kotun mai daraja ta daya a kasar nan ta tabbatar da tsohon shugaban Majalisar dattawa, Sanata David Mark a matsayin halastaccen shugaban jam'iyyar ADC ta kasa.

David Mark
Shugaban ADC na kasa, Sanata David Mark a taron kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) Hoto: Bolaji Abdullahi
Source: Twitter

Kwamitin alkalai 5 da ya saurari shari'ar rikicin ADC ne ya yanke wannan hukuncin a yau Alhamis, 30 ga watan Afrilu, 2026, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

A hukuncin da alkalan suka yanke, Kotun koli ta soke umarnin “kowa ya tsaya a matsayinsa” da Kotun Daukaka Kara da ke Abuja ta bayar a rikicin shugabancin ADC.

Wannan hukunci ya dawo da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar karkashin jagorancin David Mark, bayan da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta cire su daga rajista.

Alkalai biyar karkashin jagorancin Mohammed Lawal Garba sun ce umarnin da kotun daukaka kara ta bayar ba shi da muhimmanci.

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262