Hankali Ya Kwanta, Kotun Kolin Najeriya Ta Yanke Hukunci kan Rikicin Jam'iyyar ADC
Abuja, Nigeria - Kotun Kolin Najeriya ta yanke hukunci a karar da shigar gabanta game da rikicin shugabanci da ya addabi jam'iyyar yan hamayya ta ADC.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Kotun mai daraja ta daya a kasar nan ta tabbatar da tsohon shugaban Majalisar dattawa, Sanata David Mark a matsayin halastaccen shugaban jam'iyyar ADC ta kasa.

Source: Twitter
Kwamitin alkalai 5 da ya saurari shari'ar rikicin ADC ne ya yanke wannan hukuncin a yau Alhamis, 30 ga watan Afrilu, 2026, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
A hukuncin da alkalan suka yanke, Kotun koli ta soke umarnin “kowa ya tsaya a matsayinsa” da Kotun Daukaka Kara da ke Abuja ta bayar a rikicin shugabancin ADC.
Wannan hukunci ya dawo da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar karkashin jagorancin David Mark, bayan da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta cire su daga rajista.
Alkalai biyar karkashin jagorancin Mohammed Lawal Garba sun ce umarnin da kotun daukaka kara ta bayar ba shi da muhimmanci.
Karin bayani na nan tafe...
Asali: Legit.ng