
Labaran duniya







Fafaroma Francis ya rasu bayan fama da cutar numfashi da ya yi a Vatican. Fafaroma Francis ya bukaci a masa jana'iza mai sauki domin nuna shi bawan Allah ne.

Kotu a kasar Peru ta yanke wa tsohon shugaban kasa Humala da matarsa hukunci kan karbar rashawa daga Odebrecht domin yakin neman zabensa a 2006 da 2011.

Gwamnatin Najeriya ta rage wutar lantarkin da ta ke ba kasar Nijar da kashi 42%. An dawo ba Nijar wuta megawatt 46 maimakon 80 da ake ba kasar Nijar a baya.

Wata 'yar Najeriya mai shekaru 25 da ke rayuwa a Birtaniya ta bayyana miliyoyin da take kashewa kan kudin haya, wuta da ruwa da sauransu a kowane wata.

Saudiyya ta saka 29 ga Afrilu a matsayin ranar ƙarshe da maniyyatan Umrah za su bar ƙasar. Wanda ya karya dokar zai fuskanci hukuncin tara da daurin watanni.

Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya cire hoton Barrack Obama ya saka hoton da aka harbe shi a lokacin yakin neman zabe. Lamarin ya fara jawo suka a kasar.

China ta kara haraji kan kayayyakin Amurka zuwa 125% yayin da rikicin kasuwanci ya kara kamari. China ta ce ta shirya yin karar Amurka gaban hukumar WTO.

Gwamnatin sojan Nijar ta ayyana Hausa a matsayin harshen kasa, mataki da ke kawar da Faransanci da kuma nuna kishin yare da ikon ‘yan kasa. Amma an ce wasu na adawa.

Kasar Amurka ta yi korafi bayan Najeriya ta hana shigo da wasu kayayyakinta guda 25. Hakan na zuwa ne bayan Donald Trump ya kakaba wa Najeriya haraji.
Labaran duniya
Samu kari