Labarai
Wasu ɓarayin babura sun yi awon gaba da baburan jama'a yayin da ake tsaka da sallar tarawihi a kauyen Paso da ke ƙaramar hukumar Gwagwalada a Abuja.
Gwamna Mai Mala Buni ya amince da kashe Naira miliyan 100 na ciyar da marasa galihu abinci a kowane rana har karshen watan azumin Ramadan a jihar Yobe.
Hedkwatar tsaron Najeriya ta wallafa jerin sunayen dakarun sojojin da wasu matada suka kashe a kauyen Okuama, karamar hukumar Ughelli a jihar Delta.
Hukumar EFCC ta sake bankado da maganar karkatar da kudin makamai da ake zargin tsohon shugaban PDP, halliru Bello a mulkin tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan.
A ranar Litinin ne Shugaba Tinubu, ya mika tutar jam’iyyar APC ga dan takarar gwamnan jihar Edo na jam’iyyar, Monday Okpebholo, da abokin takararsa, Dennis Idahosa.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun tafka ta'asa a jihar Akwa Ibom. Miyaguk dauke da makamai sun shiga har cikin coci sun hallaka wanda ya kafa ta tare da babban fasto.
Gidauniyar fitaccen dan kasuwa a Afirka, Aliko Dangote ta sanar da cewa a kullum ta na ciyar da mutane fiye da 10,000 a Kano da kewaye yayin ake azumi.
Babban bankin Najeriya CBN ya kori daraktoci 7, kuma bayanai sun nuna ana shirin sake sallamar wasu ƙarin daraktoci 12 daga aiki, lamarin ya haifar da kace-nace.
Fusatattun dakarun sojoji sun kai farmaki kan maboyar shugaban 'yan ta'addan da ke da hannu a kisan da aka yi wa sojoji 16 a jihar Bayelsa. Sun kona gidaje.
Labarai
Samu kari