
Siyasa







Bayan yada jita-jitar komawar wasu gwamnonin APC zuwa tafiyar Atiku Abubakar, gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya ce ba zai taba barin jam'iyyarsa ba.

Shugaban kwamitin amintattu na jam'iyyar PDP, Sanata Adolphus Wabara, ya bayyana cewa PDP za ta ci gajiya sauyar shekar da ake yi zuwa APC a nan gaba.

Kungiyar 'yan majalisar tarayya na jam'iyyar PDP a jihar Rivers, sun nuna gamsuuwarsu kan kamun ludayin Shugaba Bola Tinubu. Za su mara masa baya a 2027.

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya gana da tsohon gwamnan Kaduna, Nasir el-Rufa'i a wani masallaci a Abuja. Haduwarsu ya kara karfafa rade radin sauya shekar Kwankwaso.

Ɗan majalisar wakilai, Ikenga Ugochinyere ya hango matsaloli a PDP inda ya gwamnoni biyu da ‘yan majalisa 40 na shirin ficewa daga PDP saboda rikice-rikice.

Hadimin Gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta a bangaren matasa da kungiyoyin farar hula, Harrison Gwamnishu ya ajiye aikinsa saboda matsalar tsaro.

Tsagin NNPP ya zargi 'yan Kwankwasiyya da jawo ficewar Sanata Kawu Sumaila da wasu jiga jigan NNPP zuwa APC. Ya nemi a yi sulhu da Rabiu Kwankwaso.

NNPP ta yi magana kan zaben 2027 inda mai magana da yawunta, Ladipo Johnson, ya ce suna nazarin yiwuwar ci gaba da zama a NNPP ko kuma shiga kawance da Atiku.

Yayin da ake zargin wasu gwamnonin PDP na shirin komawa APC, wata kungiya a jihar Osun ta shawarci Gwamna Ademola Adeleke ya goyi bayan Bola Tinubu a 2027.
Siyasa
Samu kari