Zaben Najeriya
INEC ta fitar da cikakken jerin ’yan takarar kujerun Majalisar Dattawa 109 da za a fafata a zaɓen 2027. A rahotonmu, mun kawo manyan 'yan tarakan a cikinsu.
Jam’iyyar ADC ta ce tana da yakinin kayar da APC a zaɓen 2027 idan zaɓen ya kasance cikin ’yanci da adalci, tana mai shirin kare ƙuri’un da za a kada mata.
Rikicin cikin gida na jam'iyyar ADC a Jihar Adamawa ya karu. An rantsar da ciyaman na uku, a gefe guda kuma mataimakin sakataren jam’iyyar na kasa ya murabus.
Sama da manyan malamai 600 daga jami’o’in gwamnati a Arewacin Najeriya sun bayyana goyon bayansu ga sake zaɓar Shugaba Bola Tinubu a 2027 da ake tunkara.
Dan takarar shugaban ƙasa na LPP, Chukwuemeka Nwajiuba, ya gabatar da tsarin rage wa ’yan Najeriya kuɗin wutar lantarki da man fetur idan ya lashe zaɓen 2027.
Reno Omokri ya ce Bola Tinubu zai lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027 da gagarumin rinjaye, yana mai cewa ya ƙara ƙarfafa siyasarsa tun zaben 2023.
Manyan 'yan takarar shugaban kasa a zaben 2027 da ke tafe sun yi magana kan dukiyoyinsu. Bola Tinubu, Atiku Abubakar da Peter Obi sun bayyana inda kudinsu suka fito.
Kungiyar SERAP ta bai wa hukumar INEC wa’adin kwana bakwai ta yi bayani kan yadda aka kashe sama da Naira biliyan 126 da aka ware wa harkokin zaɓe.
Sanata Victor Umeh ya ce Rabi’u Kwankwaso ba zai sha kaye a Kano a zaben 2027 ba idan an gudanar da sahihin zabe, yana mai cewa farin jininsa zai taimaka wa NDC.
Zaben Najeriya
Samu kari