Jerin Jihohin da APC za Ta Yi Zaben Fitar da Gwani bayan Gaza Yin Sasanci
Gombe, Nasarawa da wasu jihohin Najeriya za su yi zaben fitar da gwani bayan wasu masu neman takara sun ki amincewa da yarjejeniya.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
FCT, Abuja - A ranar Alhamis, 21 ga watan Mayun 2026 jam'iyyar APC ta tsara cewa za ta gudanar da zaben fitar da gwani na gwamna.
Jihohin da suka gaza cimma matsaya kan fitar da 'yan takara ta hanyar sulhu za su fafata a zaben fitar da gwani kamar yadda dokar zabe ta tanada.

Source: Facebook
A wannan rahoton, mun kawo muku jihohin da suka gaza cimma yarjeneniya wanda hakan ya tilasta jam'iyyar shirya zaben 'yar tike.
1. Za a yi 'yar tike a Gombe
Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya sanar da cewa jam'iyyar APC za ta shirya zaben fitar da gwani bayan korafe-korafe.
Hakan na zuwa ne bayan Sheikh Isa Ali Pantami da Sanata Saidu Ahmed Alkali sun ki amincewa da fitar da Jamilu Isiyaku Gwamna da jam'iyyar ta yi.

Source: Facebook
A wani sako da mai magana da yawun gwaman Gombe, Isma'ila Uba Misilli ya fitar a Facebook, ya ce jami'an tsaro sun shirya domin tabbatar da zaben ya gudana lami lafiya.
2. Yobe za ta yi zaben fitar gwani
Gwamna Mala Buni na jihar Yobe State ya ce jam’iyyar APC ta himmatu wajen gudanar da zaɓen fitar da gwani cikin ’yanci, adalci da gaskiya idan aka gaza cimma matsaya.
Rahotanni sun nuna cewa masu neman takarar gwamna shida na APC a jihar sun yi watsi da ɗan takarar da manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar suka amince da shi, Baba Wali, tare da neman a yi zabe.

Source: Facebook
Masu neman takarar sun haɗa da Ibrahim Bomoi, Bashir Machina, Kashim Musa-Tumsah, Mustapha Maihaja da Lawan Kolo.
Rahoton Punch ya nuna cewa Sanata Ahmad Lawan da tsohon sufeto janar na ’yan sanda, Mohammed Baba sun janye da batun takara a jihar.
3. Jihar Nasarawa ta bi sahu
Wasu masu neman takara a jam'iyyar APC a jihar Nasarawa sun yi watsi da dan takarar da gwamna Abdullah Sule ya amince da shi.
Tsohon sufeto janar na ’yan sanda, Mohammed Abubakar Adamu, ya tabbatar wa al’ummar ƙaramar hukumar Karu cewa yana da ƙarfin da zai iya kayar da ɗan takarar da gwamna Abdullahi Sule ke marawa baya, Sanata Aliyu Ahmed Wadada.
The Guardian ta wallafa cewa Mohammed Adamu ya ce yana da tabbacin zai yi nasara idan aka gudanar da zaɓen fitar da gwani cikin gaskiya da adalci.

Source: Twitter
4. APC za ta yi zabe a Oyo
Shugabannin jam'iyyar APC a jihar Oyo sun amince da Sharafadeen Alli a matsayin wanda zai yi mata takara a 2027, lamarin da ya samu kin amincewa daga tsohon ministan makamashi, Bayo Adelabu.
Vanguard ta wallafa cewa kin amincewar tsohon ministan ya kai ga jam'iyyar daukar matakin gudanar da zaben fitar da gwani a mako mai zuwa.

Source: Facebook
Mai neman takarar gwamna, Sharafadeen Alli ya bayyana shirinsa na shiga zaɓen fitar gwani na jam’iyyar APC kamar yadda wasu masu neman takara ke nema.
5. Ba a sasanta a Taraba ba
An yi tsammanin sauya sheƙar gwamnan Taraba Agbu Kefas daga jam’iyyar PDP zuwa APC zai share masa hanyar neman wa’adi na biyu ba tare da tangarda ba
Sai dai alamu sun nuna zai fuskanci zaɓen fitar da gwani a cikin jam’iyya mai mulki, sabanin wasu gwamnoni masu ci a wasu jihohi da suka samu amincewa a matsayin ‘yan takara su kaɗai.

Source: Facebook
Jaridar nan ta The Nation ta rahoto shugaban APC na Taraba yana cewa duk mai neman tikitin gwamna a jam'iyyarsu, kofa a bude ta ke gare shi ya fito a gwabza.
Tuni daya daga cikin masu neman takara, David Sabo Kente ya ce ba zai janye ba, zai shiga zaben tsaida gwani.
An taru a hedikwatar jam'iyyar APC
A wani labarin, mun kawo muku cewa masu neman takara sun cika sakatariyar jam'iyyar APC domin sanin sakamakon tantance su da aka yi.
Wani rahoto ya nuna cewa dole sai an yarda mutum ya tsallake tantancewa kafin ya samu damar shiga zaben fitar da gwani da za a fara a makon nan.
Wasu bayanai da Legit Hausa ta samu sun nuna cewa daga sakatariyar APC, masu neman takarar sun wuce gidan shugaban jam'iyyar a Abuja.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng



