Jihar Gombe
Jam'iyyar SDP ta sanar da hukumar INEC shirin gudanar da sabon zaben fidda gwani a Gombe da Nasarawa domin maye gurbin ’yan takarar da suka janye.
Tsohon minista Isa Ali Pantami ya sami kashi 84% na kuri'u sama da 58,000 a zabukan gwaje-gwaje na yan gizo kan zaben gwamnan jihar Gombe na 2027.
Rahotanni sun tabbatar da cewa Allah Ya yi wa Sarkin Bolari, Alhaji Ahmad Abubakar, rasuwa cikin daren nan bayan fama da rashin lafiya a birnin Gombe.
Shugaban jam'iyyar LP na Gombe, Usman Kalala, ya yi murabus ya koma PDP tare da Shehu Durbi da magoya bayansu, yana mai goyon bayan takarar Pantami.
Shugaban tsagin ADC, Nafiu Bala ya soki Atiku Abubakar bayan ya ce zai dawo da tallafin man fetur, ya ce ba shi ne ɗan takarar ADC ba a zaben 2027.
Sanata Danjuma Goje ya sake tabbatar da cewa yana cikin jam'iyyar APC, yana mai cewa ba zai sauya jam’iyya domin neman kujerar Majalisar Dattawa ba.
Yar siyasa a Najeriya, Naja'atu Mohammaed ta musanta rahotannin da ke yawo cewa ta tura tawaga ta musamman domin ba Farfesa Isa Ali Pantami hakuri.
Sanata Muhammad Danjuma Goje ya ce har yanzu yana cikin APC, amma yana tuntubar mutane kan matakin siyasar da zai ɗauka a 2027, bayan rashin samun tikitin APC.
Tsohon gwamnan Gombe, Sanara Danjuma Goje, ya musanta ficewa daga APC duk da rashin bayyana sunansa a jerin hukumar INEC na ‘yan takarar zaben 2027.
Jihar Gombe
Samu kari