"Za Ka Sha Kaye"; Dan Takarar ADC Ya Yi Wa Gwamna Abba Barazana kan 2027

"Za Ka Sha Kaye"; Dan Takarar ADC Ya Yi Wa Gwamna Abba Barazana kan 2027

  • Ibrahim Alamin Little da ke takarar gwamnan jihar Kano a inuwar jam'iyyar ADC, ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf zai sha kaye a zaɓen 2027
  • Ɗan takarar na ADC ya kuma bayyana Abdulkadir Shehu Bari a matsayin abokin takararsa a zaben shekarar 2027 da ake tunkara
  • Ibrahim Alamin Little ya yi alƙawarin mayar da hankali kan ilimi, lafiya da bunƙasa matasa idan ya samu damar zama gwamna

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Kano – Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kano, Alhaji Ibrahim Alamin Little, ya gargadi Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Alhaji Ibrahim Alamin Little ya gargadi Gwamna Abba da ya shirya barin gidan gwamnati, yana hasashen cewa zai sha kaye a zaɓen gwamna na 2027.

Little ya yi wa Abba barazana kan zaben 2027
Gwamna Abba Kabir Yusuf da Hon Ibrahim Alamin Little Hoto: Isah Muhammad Salisu, Hon. Ibrahim Ali Amin-Little
Source: Facebook

Little ya bayyana haka ne a Kano yayin wani taron manema labarai, inda ya sanar da Abdulkadir Shehu Bari daga ƙaramar hukumar Rogo a matsayin abokin takararsa a zaɓen 2027, cewar rahoton jaridar Tribune.

Kara karanta wannan

2027: Matawalle ya fito fili ya bayyana irin zaben da za a yi karkashin gwamnatin Tinubu

Ya zargi gwamnatin Abba Kabir Yusuf da gudanar da ayyuka ta hanyar abin da ya kira “window dressing”, yana mai cewa al’ummar jihar na buƙatar gwamnati mai iya magance matsalolin da suke fuskanta.

A cewarsa, masu zaɓe za su cire gwamnatin mai ci daga mulki a 2027 saboda ƙara nuna damuwa kan matsalar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi, ilimi, kiwon lafiya da fannin noma.

Little ya soki gwamnatin Kano

Little ya nuna damuwa musamman kan ƙaruwa da ake samu na matasan da ke safarar miyagun ƙwayoyi da kuma shaye-shayensu, yana mai bayyana shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a matsayin ɗaya daga cikin manyan matsalolin da jihar ke fuskanta.

Ya kuma soki gwamnatin kan abin da ya bayyana a matsayin rashin isasshen kulawa ga ilimi da kiwon lafiya, da kuma ƙarancin tallafin da ake bai wa manoma.

Ɗan takarar na ADC ya ce noma shi ne ginshiƙin tattalin arzikin Kano, amma ya ce manoma na buƙatar samun takin zamani, kayan aiki da sauran abubuwan da ake amfani da su wajen noma cikin sauƙi domin ƙara yawan amfanin gona.

Kara karanta wannan

Ana shirin sauya dan takarar gwamnan PDP a Benue? Gaskiya ta fito

Dan takarar ADC ya yi alkawura

Little ya yi alƙawarin cewa idan aka zaɓe shi, gwamnatinsa za ta ba da fifiko ga ilimi, kiwon lafiya, bunƙasa matasa da kuma ƙarfafa mata.

Ya kuma yi alƙawarin magance matsalar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi tare da samar da shirye-shiryen jin daɗin jama’a ga masu rauni, ciki har da zawarawa, marayu da yaran da ba sa zuwa makaranta.

"Da zarar an shigar da mu gidan gwamnatin Kano bayan zaɓen 2027, za mu tabbatar mun magance matsalolin da suka addabi ɓangaren kiwon lafiya tare da samar da ingantattun shirye-shiryen jin daɗin jama’a ga masu rauni a cikin al’umma.” In ji shi.

Little ya samu abokin takara
Ibrahim Alamin Little na daga hannun abokin takararsa a zaben 2027 Hoto: Hon Ibrahim Ali Amin-Little
Source: Facebook

Ya yi alƙawarin sauya tsarin mulki

Little ya ƙara yin alƙawarin sake fasalin tsarin gudanar da gwamnati baki ɗaya domin tabbatar da samun dama iri ɗaya ga ’yan ƙasa ba tare da la’akari da matsayinsu ko asalinsu ba.

Ya ce gwamnatinsa za ta bunƙasa kirkire-kirkire da harkokin kasuwanci ta hanyar kafa cibiyoyin tattalin arziki a sassa daban-daban.

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: Buba Galadima ya siffanta Bala Mohammed da rabin gwamna

A cewarsa, shirin zai taimaka wajen sauya Kano daga al’ummar da ta fi dogaro da saye da amfani da kayayyaki zuwa tattalin arziki mai samar da kayayyaki, wanda zai samar da ayyukan yi, ƙara arziki da kuma inganta rayuwar mazauna jihar.

An karrama Gwamna Abba

A wani labarin kuma, kun ji cewa kungiyar mata yan jarida ta Najeriya (NAWOJ) ta karrama Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, da lambar yabo kan zaman lafiya, tsaro da shugabanci nagari.

Bayanai sun nuna cewa an ba gwamnan lambar yabon ne saboda irin ci gaban da gwamnatin sa ke samarwa a jihar Kano daga watan Mayun 2023.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng