Jihar Yobe
Sarkin Potiskum ya ce amfani da ƙarfin soja kaɗai ba zai kawo ƙarshen rashin tsaro a Najeriya ba, yana mai kira ga gwamnati ta magance talauci da rashin adalci.
Shugabar Mata ta APC a Yobe, Fatima Mairiga, ta rasu bayan gajeriyar rashin lafiya a Kano, inda aka sanar da gudanar da jana’izarta a birnin Damaturu.
Gwamnatin Yobe ta amince da kashe Naira miliyan 460.83 domin tallafa wa mata masu ƙananan sana'o'i, musamman masu soya ƙosai, da kayayyakin aikin sana'a.
Mutum uku sun rasu bayan wata guguwa mai ƙarfi ta afkawa Gashua a jihar Yobe, inda ta lalata ɗaruruwan gidaje da kadarori. Hukumar YOSEMA ta fara tantance barnar.
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba da umarnin yi wa Sanata Ahmad Lawan isar da takardun ƙara ta hanyar madadin, bayan an kasa same shi kai tsaye.
Gwamna Mai Mala Buni ya amince da ɗaukar nauyin tawagar Yobe zuwa taron Arewa Media Summit a Kano, inda mahalarta za su tattauna makomar yaɗa labarai.
Kamfanin TCN ya sanar da cewa jihohi biyar za su fuskanci matsalolin wutar lantarki, sun hada da Kano, Bauchi, Yobe, Jigawa da Katsina da yankin kasar Nijar.
Hukumar NEMA ta kaddamar da rabon kayan abinci da cbiyar Sarki Salman ta kawo Najeriya domin a rabawa talakawa a jihohi biyar na kasar nan da suka shiga damuwa.
Yarima Ibn Mahmud ya zama sabon Sarkin Ngazargamu bayan rasuwar mahaifinsa. Gwamnan Yobe, Mai Mala Buni ne ya sanar da nada shi a ranar Juma'a, 12 ga Yunin 2026.
Jihar Yobe
Samu kari