Kano da Wasu Jihohin Arewa 4 da Zaben Gwamna Zai Dauki Hankali a 2027

Kano da Wasu Jihohin Arewa 4 da Zaben Gwamna Zai Dauki Hankali a 2027

Yayin da zaben 2027 ke kara kusantowa, gwamnonin da za su kammala wa'adi na farko sun fara shirye-shiryen neman tazarce domin yin zango biyu kamar yadda dokar Najeriya ta tanada.

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Sai dai wasu gwamnonin na fuskantar kalubale mai girma a kokarinsu na neman wa'adi na biyu saboda bata wa da iyayen gidansu da kuma wasu malamai da suka shigo siyasa.

Gwamna Abba.
Gwamna Abba Kabir Yusuf a wani taron raba wa mata jari a fadar gwamnatin Kano Hoto: Sanusi Bature D-Tofa
Source: Facebook

Gwamna Abba zai fuskanci kalubale a 2027

Kano na daya daga cikin wadannan jihohi da za su fi daukar hankali sakamakon rabuwar Gwamna Abba Kabir Yusuf da uban gidansa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, kamar yadda Daily Trust ta rahoto.

Yayin da Gwamna Abba ya koma APC kuma yake shirin neman tazarce a 2027, madugun Kwankwasiyya ya hade da manyan 'yan adawa a ADC domin karbe mulkin Kano a zabe mai zuwa.

Kara karanta wannan

Atiku ya tono 'babbar matsala' kan kada kuri'a a 2027, ya ce za a yi magudi

Jihohi 5 da zaben su zai dauki hankali

Irin wadannan kalubale da wasu dalilai ne suka sanya zaben gwamnan Kano da wasu jihohin Arewacin Najeriya za su dauki hankali matuka, kuma za a zuba ido aka abin da zai faru a 2027.

A wannan rahoton, Legit Hausa ta tattaro muku jihohin da ake hasashen za su dauki hankalin Najeriya a zaben gwamnonin da za a yi ranar 6 ga watan Fabrairun 2027.

1. Jihar Kano

Kano ita ce a sahun farko a jihohin Arewa da ake ganin zabeen gwamna da za a yi a 2027 zai yi zafi kuma zai dauki hankali matuka.

A zaben 2023, Gwamna Abba Kabir Yusur na NNPP, wanda ke tare da Kwankwaso a lokacin, ya kayar da dan takarar jam'iyya mai mulki, APC, Dr. Nasir Yusuf Gawuna.

Sai dai a yanzu, Abba ya bar gidan Kwankwaso, ya koma tsagin tsohon shugaban APC na kasa, Dr. Abdullahi Ganduje, yayin da Gawuna ya koma tafiyar Kwankwasiyya, cewar rahoton Guardian.

Kara karanta wannan

Dalilan da suka sanya Abba zabar Garo a mataimakin gwamnan Kano

Abba da Kwankwaso.
Gwamna Abba Kabir Yusuf da madugun Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso a masallaci wurin daura aure Hoto: Abba Kabir Yusuf
Source: Facebook

Bisa wannan sauye-sauye da aka samu, ana ganin zaben gwamnan Kano na 2027 zai dauki hankali matuka saboda yadda Gwamna Abba zai kara da dan takarar da Kwankwaso zai marawa baya.

2. Jihar Kaduna

Gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani na daya daga cikin gwamnonin Arewa da ake ganin za su fuskanci kalubale wajen neman tazarce a zaben 2027.

Rahoton The Nation ya nuna cewa hakan yana da nasaba da raba gari da gwamnan ya yi da uban gidansa, tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai.

El-Rufai ya hada kai da manyan jagororin adawar Najeriya kamar Atiku Abubakar da Peter Obi, domin kalubalantar gwamnatin APC a zaben 2027.

Duk da ADC na fama da rikicin cikin gida, amma ana ganin zaben Kaduna zai dauki hankali fiye da yadda ya faru a 2023 saboda rabuwar Gwamna Uba Sani da El-Rufai.

Uba Sani da El-Rufai.
Gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani da magabacinsa, Nasir Ahmad El-Rufai Hoto: Uba Sani, @elrufai
Source: Facebook

3. Jihar Gombe

Tuni siyasar jihar Gombe ta fara daukar hankali a Arewacin Najeriya bayan babban malamin addinin musulunci kuma tsohon ministan sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami ya nuna sha'awar takara.

Kara karanta wannan

Ministan makamashi na shirin ajiye aiki, zai shiga takarar gwamna a 2027

Takarar da Isa Pantami ke shirin fitowa a inuwar APC ta ja hankalin yan Arewa, musamman ganin cewa ba a saba ganin manyan malamai kamarsa suna neman kujerar mulki ta gwamna ba.

Duk da dai har yanzu APC ba ta yanke wanda za ta ba tikitin takarar gwamnan Gombe a 2027 ba, mutane sun zuba ido su ga yadda za ta kaya a zabe mai zuwa a jihar.

Jaridar Punch ta ruwaito Pantami na cewa ayyukan da ya gudanar a lokacin da yake kan muƙamin gwamnati su ne za su ba da shaidar cancantarsa a zaɓen 2027.

Sheikh Pantami.
Tsohon ministan sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami lokacin da yake yankar katin zama cikakken dan APC s jihar Gombe Hoto: Abba Pantami
Source: Twitter

4. Jihar Sakkwato

Wani abu da ya kara jan hankalin mutane a siyasar Arewacin Najeriya, shi ne ayyana fitowa takarar gwamnan da Sheikh Bashir Sani Sokoto ya yi.

Malamin Musulunci ya bayyana haka ne a wani wa'azi da ya gabatar, wanda Taskar Malaman Sunnah TV ta wallafa a shafin YouTube.

Wannan lamari ya girgiza siyasar jihar Sakkwato, kuma malamin wanda ake ganin yana da mabiya da yawa, zai fafata da gwamna mai ci, Ahmed Aliyu na jam'iyyar APC.

Kara karanta wannan

Murtala Garo: Abubuwan sani game da mai iya zama sabon mataimakin gwamnan Kano

Sheikh Bashir Ahmad.
Babban malamin addinin Musulunci, Sheikh Bashir Ahmad Sani Sokoto Hoto: Sheikh Bashir Ahmad Sani Sokoto
Source: Facebook

A daya bangaren kuma, jam'iyyar ADC da ake tunanin malamin zai shiga, karkashin jagorancin Sanata Aminu Waziri Tambuwal, na shirye-shiryen ganin ta karbe mulkin Sakkwato a 2027.

5. Jihar Zamfara

Sauya shekar Gwamna Dauda Lawal daga PDP zuwa APC da fitowa takarar malamin addinin musulunci, Sheikh Abdulmutallib Gusau, sun sa siyasar jihar Zamfara ta fara daukar hankali a wannan karon.

Gwamnan ya koma APC tare da hadewa da Karamin ministan tsaro, Bello Matawalle, wanda har yanzu yana da damar sake neman takarar gwamna kamar yadda doka ta tanada.

A rahoton jaridar Guardian, malamin addinin Musulunci, Sheikh Abdulmutallib Gusau, ya shiga cikin sahun mutanen da ke son fafatawa da Gwamna Dauda Lawal a zaben 2027.

Gwamna Lawal.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal yayin wani zama da kwamishinoni a gidan gwamnati da ke Gusau Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Sheikh Abdulmutallib ya ce matakin da ya ɗauka na shiga siyasa duk da matsayinsa na malamin addini, ya biyo bayan yadda abubuwa ba sa tafiya daidai a ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Kotu ta ɗauki mataki kan buƙatar belin El Rufai, Malam zai zauna a hannun ICPC

Sakamakon haka, ana ganin zaben Zamfara zai dauki hankali duba da manyan jiga-jigan da za su iya neman tikitin APC da kuma takarar shehin, wanda tuni ya shiga ADC.

Da gaske an hana Pantami takara a Gombe?

A wani rahoton, kun ji cewa tsohon ministan sadarwa, Sheikh Isa Pantami ya musanta rahotannin da ake yadawa cewa Gwamna Inuwa Yahaya ya nemi ya hakura da takarar gwamna a Gombe.

An yada wasu rahotanni masu ikirarin cewa Gwamna Inuwa Yahaya ya bukaci Farfesa Pantami da ya hakura da batun yin takara a zaben 2027.

Sai dai, Farfesan ya fito ya ƙaryata wannan labari gaba ɗaya, inda ya bayyana cewa ko kadan babu kamshin gaskiya a cikinsa.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262