Abun Bakin ciki: Yadda 'Yan Fashi Suka Kashe Dalibar Ajin Karshe a Jami'ar Lafia
- Iyali, abokai da al'ummar Jami'ar FULAFIA sun yi jana'izar Habiba Ummi Lele da aka harbe har lahira yayin dawowa daga bikin yaye ɗalibai
- Mutuwar ɗalibar ta ƙara tayar da hankula kan matsalar tsaro a Nasarawa, bayan sace wasu ɗalibai uku na jami'ar kwanaki kaɗan da suka gabata
- 'Yan Najeriya sun cika kafafen sada zumunta da saƙonnin ta'aziyya da kira ga gwamnati ta ɗauki matakan inganta tsaro
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da takwas a aikin jarida
Nasarawa - An yi jana'izar ɗalibar aji na 400 a sashen ilmin sinadarai na Jami'ar Tarayya da ke Lafia (FULAFIA), Habiba Ummi Lele, wadda ake zargin 'yan fashi da makami sun kashe a jihar Nasarawa.
Habiba ta rasa ranta ne a ranar Asabar bayan wasu da ake zargin 'yan fashi da makami ne suka buɗe wa motar da take ciki wuta yayin da take dawowa Lafia daga bikin yaye wata kawarta a Kwalejin Kiwon Lafiya da Fasaha da ke Keffi.

Source: Facebook
Jana'izar dalibar da aka kashe
An gudanar da jana'izar Habiba a ranar Lahadi a gidan ɗan majalisar dokokin jihar Nasarawa mai wakiltar mazabar Awe ta Arewa, Hon. Hudu A. Hudu Kanje, da ke garin Kanje, in ji rahoton Daily Trust.
Shugaban ƙaramar hukumar Awe, Hon. Umar Abubakar Dan'Akano, da Hon. Hudu Kanje na daga cikin manyan jami'an da suka halarci sallar jana'izar.
Iyalan marigayiyar, abokanta, shugabannin al'umma da sauran masu alhini sun taru domin yi mata addu'a tare da jajanta wa iyalanta bisa wannan babban rashi.
Mutuwar dalibar ta girgiza 'yan Najeriya
Mutuwar Habiba ta jawo jimami a kafafen sada zumunta, inda 'yan Najeriya da dama suka bayyana alhininsu tare da nuna damuwa kan yadda matsalar tsaro ke ƙara ta'azzara.
Wani mai amfani da Facebook, Mujahid Saleh Saad, ya yi addu'ar Allah Ya gafarta mata, Ya ba iyalanta, abokanta da al'ummar FULAFIA haƙurin jure wannan rashi.
A nata ɓangaren, Stephiny Ugomma ta bayyana takaicinta, tana mai cewa samun labari mai daɗi a Najeriya a yanzu ya zama abin godiya.
Shi ma Tony Ocheni ya yi Allah wadai da matsalar tsaro, yana mai cewa yawan mutanen da ake kashewa a Najeriya ya zarce na wasu ƙasashen da ke fama da yaƙi.
An sake kira a ƙara tsaro
Mutuwar Habiba ta zo ne kwanaki kaɗan bayan da wasu da ake zargin 'yan bindiga ne suka sace ɗalibai uku na matakin 100 na FULAFIA daga wani masaukin ɗalibai da ke Bukan Kwato a Lafia.

Source: Original
Rahotanni sun ce maharan sun kai harin ne da daddare, inda suka tafi da ɗaliban, lamarin da ya ƙara tayar da fargaba kan tsaron ɗaliban da ke zaune a wajen harabar jami'a.
Waɗannan hare-hare guda biyu sun sa ɗalibai, iyaye da mazauna jihar suka sake yin kira ga jami'an tsaro da gwamnatin jihar Nasarawa da su ɗauki matakan gaggawa domin kare rayuka da dukiyoyin al'umma.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, hukumomi ba su fitar da wata sanarwa kan harin da ya yi sanadin mutuwar Habiba ba, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin ceto ɗaliban da aka sace.
Asali: Legit.ng

