Jerin Jihohin da APC, APGA da Sauran Jam'iyyu ke Mulki gabanin Zaben Gwamnan Ekiti

Jerin Jihohin da APC, APGA da Sauran Jam'iyyu ke Mulki gabanin Zaben Gwamnan Ekiti

Ado-Ekiti, Ekiti – Cikin ƙasa da sa’o’i 24 masu zuwa, al’ummar Ekiti za su fita rumfunan zaɓe ranar Asabar, 20 ga Yunin 2026, domin zaɓen wanda zai zama gwamnan jihar na gaba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Gwamna mai ci, Biodun Oyebanji na jam’iyyar APC, na neman sake wa’adin mulki na biyu a wannan zabe, wanda ake ganin zai ja hankalin yan Najeriya.

Gwamn Oyebanji.
Gwamnan jihar Ekiti, Biodun Oyebanji a wurin yakin neman zaben APC Hoto: Biodun Oyebanji
Source: Facebook

APC na neman tazarce a jihar Ekiti

Gwamna Oyebanji zai fafata da wasu ‘yan takara 13 masu neman karɓe masa kujerar gwamna, kamar yadda jaridar Premium Times ta ruwaito.

Ko da yake akwai ‘yan takara 14 a zaɓen, manyan yan takarar da ake ganin za su iya yin tasiri sun haɗa da Gwamna Biodun Oyebanji na APC da Dakta Wole Oluyede na PDP da Dare Bejide na jam'iyar ADC.

Kara karanta wannan

An jibge jami'an tsaro, sun hana mutane zirga zirga a kananan hukumomi 2 a jihar Kano

Yayin da ake shirin zaben gwamnan Ekiti na gaba, Legit Hausa ta tattaro muku jihohin da APC da sauran jam'iyyun siyasa ke mulki a Najeriya. Ga su kamar haka.

Jihohin da APC ke mulki

Tashar TVC News ta ruwaito cewa jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya na da jihohi 31 da ke karkashinta bayan sauya shekar da wasu gwamnonin PDP suka yi bayan zaben 2023

1. Adamawa – Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

2. Akwa Ibom – Gwamna Umo Eno

3. Bayelsa – Gwamna Duoye Diri

4. Benue – Gwamna Hyacinth Alia

5. Borno – Gwamna Babagana Zulum

6. Cross River – Gwamna Bassey Otu

7. Delta – Gwamna Sheriff Oborevwori

8. Ebonyi – Gwamna Francis Nwifuru

9. Edo – Gwamna Monday Okpebholo

10. Ekiti – Gwamna Biodun Oyebanji

11. Enugu – Gwamna Peter Mbah

12. Gombe – Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya

13. Imo – Gwamna Hope Uzodinma

14. Jigawa – Gwamna Umar Namadi

15. Kaduna – Gwamna Uba Sani

16. Kano – Gwamna Abba Kabir Yusuf

17. Katsina – Gwamna Dikko Umaru Radda

Kara karanta wannan

Dalilan da za su iya sanyawa PDP ta sha kashi a zaben gwamnan Ekiti na 2026

18. Kebbi – Gwamna Nasir Idris

19. Kogi – Gwamna Ahmed Usman Ododo

20. Kwara – Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq

21. Lagos – Gwamna Babajide Sanwo-Olu

22. Nasarawa – Gwamna Abdullahi Sule

23. Niger – Gwamna Mohammed Umar Bago

24. Ogun – Gwamna Dapo Abiodun

25. Ondo – Gwamna Lucky Aiyedatiwa

26. Plateau – Gwamna Caleb Mutfwang

27. Rivers – Gwamna Siminalayi Fubara

28. Sokoto – Gwamna Ahmad Aliyu

29. Taraba – Gwamna Agbu Kefas

30. Yobe – Gwamna Mai Mala Buni

31. Zamfara – Gwamna Dauda Lawal.

Tutar APC.
Tutar jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya Hoto: @OfficialAPCNig
Source: Twitter

Wace jihar ke hannun jam'iyyar APGA?

Jihar Anambra da ke yankin Kudu maso Gabashin Najeriya ce kaɗai jam’iyyar APGA ke mulki, ƙarƙashin Gwamna Charles Chukwuma Soludo.

Gwamna Soludo ya koma wa'di na biyu ne bayan sake lashe zabe a ranar 8 ga Nuwamba, 2025, a karkashin jam'iyyar APGA, kamar yadda BBC ta ruwaito.

Jihohin da APM ke mulki

Jam’iyyar adawa ta APM na da jihohi biyu da ke ƙarƙashin mulkinta, wadanda dukansu suka fito daga jam'iyyar PDP.

Kara karanta wannan

Ekiti 2026: Manyan 'yan takara 3 da ake ganin za su iya samun nasara a zaben

1. Bauchi – Gwamna Bala Mohammed

2. Oyo – Gwamna Seyi Makinde

Jihar da jam'iyyar Accord ke mulki

Jihar Osun ce kaɗai jam’iyyar Accord Party ke mulki, ƙarƙashin Gwamna Ademola Adeleke, wanda ya bar jam'iyyar PDP saboda rigingimun cikin gida.

Gwamna Adeleke na neman tazarce zuwa zango na biyu a zaben gwamnan jihar Osun, wanda za a gudanar ranar 15 ga watan Agusta, 2026, cewar rahoton Guadian.

Jam'iyyar LP na mulki a jiha 1

Kamar dai jam'iyyun Accord da APGA, jihar Abia ce kaɗai jam’iyyar LP ke mulki, inda Gwamna Alex Otti ke jagoranci.

Gwamna Alex Otti ya karbi mulkin Abia ne bayan nasarar da ya samu a zaben 2023, lokacin LP ta ba da mamaki saboda tasirin dan takararta na shugaban kasa, Peter Obi.

Alex Otti.
Gwamnan jihar Abia, Alex Otti yana magana a fadar gwamnatinsa Hoto: Alex C. Otti
Source: Facebook

Ekiti: Dalilan da za su jawo faduwar PDP

A wani rahoton, kun ji cewa jam'iyyar PDP na ciki jam'iyyun siyasada za su gwabza a zaben gwamnan jihar Ekiti ranar Asabar, 20 ga watan Yuni, 2026.

Kara karanta wannan

2026: Manyan abubuwa 3 da za su iya kawo wa APC cikas a zaben gwamnan Ekiti

Wole Oluyede, wanda likitan lafiya ne, ya zama ɗan takarar PDP a watan Nuwamba na shekarar 2025 bayan ya sami ƙuri'u 279 a zaɓen fitar da gwani.

Jam'iyyar PDP ta fuskanci matsaloli gabanin zaben Ekiti, wadanda ake ganin za su iya kawo mata gangarda ko ma ga sha kasa a zaben.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262