Jerin Gwamnonin Jihar Ekiti daga 1999 zuwa Yau yayin da Ake Shirin Sabon Zabe a 2026

Jerin Gwamnonin Jihar Ekiti daga 1999 zuwa Yau yayin da Ake Shirin Sabon Zabe a 2026

A ranar Asabar mai zuwa, 20 da watan Yuni, 2026 ne za a gudanar da zaben gwamnan jihar Ekiti da ke yankin Kudu maso Yammacin Najeriya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Tuni dai hukumar zaben Najeriya mai zaman kanta (INEC) ta fara aiwatar da shirye-shiryen gudanar da wannan zabe cikin lumana da bin ka'idojin da doka ta tanada.

Oyebanji.
Gwamna Biodun Oyebanji da tsofaffin gwamnonin Ekiti, Ayo Fayose da Otunba Niyi Adebayo Hoto: Biodun Oyebanji, Ayo Fayose, Otunba Niyi Adebayo
Source: Facebook

Tashar Channels tv ta ruwaito cewa INEC ta fara rabon muhimman kayayyakin zabe ranar Alhamis, 18 ga watan Yuni, 2026 duk a wani bangare na ganin zaben ya gudana lafiya.

Sai dai yayin da shirye-shirye suka yi nisa, Legit.ng Hausa ta tattaro muku jerin gwamnonin da suka mulki jihar Ekiti tun daga dawowar mulkin dimokuradiyya a 1999 zuwa yau.

1. Otunba Niyi Adebayo

A rahoton da Gwamnatin Ekiti ga wallafa shafin yanar gizo, Niyi Adebayo ne gwamnan farar hula na farko da aka zaba a jihar bayan dawowar dimokuradiyya a Najeriya a shekarar 1999.

Kara karanta wannan

An fallasa shirin shawo kan talaka da shinkafa da taliya a zaben gwamnan Ekiti

Adebayo ya karbi mulki a ranar 29 ga Mayu, 1999 bayan nasarar da ya samu karkashin inuwar jam'iyyar AD, kuma ya kammala wa’adinsa na shekaru hudu.

Adebayo.
Ministan masana'antu kuma tsohon gwamnan jihar Ekiti, Otunba Niyi Adebayo Hoto: Otunba Niyi Adebayo
Source: Facebook

2. Ayodele Fayose

Ayo Fayose na jam'iyyar PDP ne ya zama gwamna na biyu da aka zaba ta hanyar dimokuradiyya a Jihar Ekiti a ranar 29 ga Mayu, 2003.

Amma wa'adin mulkinsa ya kare kafin lokacinsa a ranar 16 ga Oktoba, 2006, sakamakon tsige shi da majalisar dokokin jihar ta yi saboda zargin aikata ba daidai ba, kamar yadda The Nation ta kawo.

Fayose.
Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose Hoto: Ayo Fayose
Source: Facebook

Tsige Fayose da Majalisar Dokokin Jihar Ekiti ta yi a ranar 16 ga Oktoba, 2006, ya samo asali ne daga zargin yin sama-da-fadi da dukiyar gwamnati, kura-kurai wajen bada kwangiloli, da kuma hannu a tashe-tashen hankula na siyasa

3. Janar Tunji Olurin (Mai Ritaya)

Bayan ayyana dokar ta-baci a jihar Ekiti, tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo ya nada Birgediya Janar Tunji Olurin mai ritaya a matsayin mai gudanar da harkokin jihar.

Shugaba Obasanjo ya yi haka ne domin dawo da zaman lafiya da daidaito kafin gudanar da sabon zabe, inda shugaban rikon ya yi mulki daga ranr 19 ga Oktoba, 2006 zuwa 27 ga Afrilu, 2007.

Kara karanta wannan

Ficewar Pantami daga APC ta bar baya da kura, jam'iyyar ta fitar da sabon bayani

4. Cif Tope Ademiluyi

Tope Ademiluyi ya karbi gudanar da harkokin jihar Ekiti a matsayin mukaddashin gwamna daga ranar 27 ga watan Afrilu, 2007 zuwa ranar 29 ga Mayu, 2007

Ya jagoranci harkokin jihar na wani dan gajeren lokaci kafin sabuwar gwamnatin da aka zaba ta karbi mulki.

5. Segun Oni

Segun Oni na jam'iyyar PDP ya hau mulkin jihar Ekiti bayan nasarar da ya samu a babban zaben 2007. Sai dai Kayode Fayemi ya kalubalanci sakamakon zaben a kotu.

A rahoton Vanguard, bayan shekaru uku ana shari’a, Kotun Daukaka Kara da ke Ilorin ta soke nasararsa a ranar 15 ga Oktoba, 2010, bayan ta gano kura-kurai da suka shafi gudanar da zaben.

Segun.
Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Mista Segun Oni Hoto: Segun Oni
Source: Facebook

6. Tunji Odeyemi

Bayan kotun daukaka kara ta sauke Segun Oni, Tunji Odeyemi ya karbi ragamar mulki a matsayin mukaddashin gwamna daga ranar 17 ga Fabrairu, 2009 zuwa 6 ga Mayu, 2009

Ya jagoranci harkokin gwamnatin Ekiti a lokacin sauyin mulki da ya biyo bayan hukuncin kotu da rigingimun siyasa.

Kara karanta wannan

An kuma dage shari'ar tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El Rufai

7. Kayode Fayemi

Kayode Fayemi ya zama gwamna bayan hukuncin kotu ya tabbatar da shi a matsayin wanda ya lashe zaben da aka yi takaddama a kansa.

Fayemi ya kammala wa'di daya a kan mulki daga ranar 16 ga Oktoba, 2010 zuwa 16 ga Oktoba, 2014, inda ya sauka daga mulki bayan ya sha kaye a zaben Ekiti na 2014.

Fayemi.
Tsohon gwamnan jihar Ekiti kuma tsohon ministan ma'adanai, Kayode Fayemi Hoto: @Kfayemi
Source: Twitter

8. Ayo Fayose

Fayose ya dawo kan mulki karo na biyu bayan ya kayar da Fayemi a zaben gwamnan jihar Ekiti na shekarar 2014, kamar yadda Premium Times ta ruwaito.

Nasarar da Fayose ya samu a karkashin inuwar PDP a shekarar 2014 a kan gwamna mai ci, Fayemi ta fuskanci ƙalubale a kotu amma an tabbatar da hakan.

9. Kayode Fayemi

Fayemi, wanda ya yi murabus daga kujerar ministan ma'adanai a gwamnatin marigayi Muhammadu Buhari, ya sake komawa kan mulki a jihar Ekiti a zaben gwamna na 2018.

Ya samu wannan nasara ne karkashin inuwar jam'iyyar APC mai mulki, inda ya gaji Fayose daga ranar 16 ga Oktoba, 2018 zuwa 16 ga Oktoba, 2022.

Kara karanta wannan

Bincike: 'Yan bindiga ne suka mika gawar Janar Rabe hannu da hannu? Gaskiya ta fito

9. Biodun Oyebanji

Gwamna Biodun Oyebanji na jam'iyyar APC shi ne Gwamnan jihar Ekiti mai ci, wanda ya gaji Kayode Fayemi bayan zaben da aka gudanar a shekarar 2022.

Daily Trust ta ce Oyebanji ya karbi mulki a ranar 16 ga watan Oktoba, 2022 karkashin inuwar APC kuma a halin yanzu yana daga cikin yan takarar da za su fafata a zaben ranar Asabar mai zuwa.

Oyebanji.
Gwamnan jihar Ekiti da ke neman tazarce a zaben 2026, Biodun Oyebanji Hoto: Biodun Oyebanji
Source: Twitter

INEC ta yi alkawari kan zaben Ekiti

A wani labarin, kun ji cewa shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC, Farfesa Joash Amupitan ya ce kuri’un masu zabe za su yi tasiri a zaben gwamnan jihar Ekiti.

Farfesa Amupitan ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar tantance shirye-shiryen zabe da ya kai jihar Ekiti tare da sauran kwamishinonin INEC gabanin zaben gwamna mai zuwa.

A cewarsa, cikin manyan ayyuka tara da hukumar INEC ta tsara domin zaben gwamnan Ekiti, an kammala guda bakwai.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262