
Zaben jihohi







Jam'iyyar LP na ci gaba da rasa jiga-jiganta ga APC da PDP, ciki har da Valentine Ozigbo, dan takarar gwamna, wanda ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar a Anambra.

Valentine Ozigbo ya koma APC daga LP, yana neman takarar gwamna a Anambra. Bashir Ahmad ya ce jam’iyyun adawa za su rushe kafin nan da babban zaben 2027.

PDP ta fara sayar da fom ɗin takarar gwamnan Anambra, zaɓen fidda gwani zai gudana 5 ga Afrilu, yayin da za a mika sunan ɗan takara zuwa ga INEC a ranar 22 ga Mayu.

Majalisar wakilai ta saurari bukatar kirkirar sababbin jihohi uku: Oke-Ogun, Ijebu da Ife-Ijesa daga Hon. Oluwole Oke. Majalisar ta tattauna kan muhimman kudurori.

Hukumar zabe ta kasa (INEC) ta kalubalanci tsohon kwamishinan zaben jihar Adamawa, Hudu Ari ya kare kansa a gaban kotu kan zarge-zargen da ya gabatar.

Kungiyar kwadago ta Najeriya watau NLC ta nuna damuwa kan yadda gwannoni ke barin jihohinsu su tafi Abuja duk da halin ƙuncin rayuwar da jama'arsu ke ciki.

Tun ana saura kusan shekara biyu siyasar jihar Kano ta soma daukar zafi. Yayin da Abba zai iya neman tazarce a 2027, akwai 'yan siyasa 5 da za su iya ba shi matsala.

Bayan korarsa daga aiki da Bola Tinubu ya yi, tsohon kwamishinan INEC a jihar Adamawa, Hudu Ari, ya jaddada cewa Sanata Aisha Binani ce ta lashe zaben gwamna.

Ana zargin wani Farfesa a Akwa Ibom da yada sakamakon zaben da aka gudanar a shekarar 2019 inda kotu a Uyo ta yanke hukuncin daurin shekaru uku kansa.
Zaben jihohi
Samu kari