Zaben jihohi
Tawagar yakin neman zaben Ademola Adeleke ta yi barazanar kai karar Sanata Francis Fadahunsi kan zargin bata suna, inda ta bukaci Naira biliyan 10 a matsayin diyya.
Wani Sanata daga jihar Osun ya jawo ce-ce-ku-ce bayan an zarge shi da umartar magoya baya su kashe ’yan jam’iyyar Accord gabanin zaben gwamnan jihar.
Zaben Osun: Adeleke ya ce ba ya tsoron karfin gwamnatin tarayya ko goyon bayan gwamnoni ga APC, yana mai cewa a shirye yake ya fafata a zaben Asabar.
Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke, ya ce rawa ba ta hana shi aiki, yana mai cewa ya gina hanyoyi tare da gyara cibiyoyin lafiya sama da 200 a jihar.
Dan takarar shugaban kasa na ADC, Atiku Abubakar ya nemi al'ummar Osun su zaɓi Najeem Salaam na ADC, yana cewa mafi kyawun ‘yan Najeriya suna cikin jam'iyyar.
Ɗan takarar APGA a zaɓen gwamnan Osun, Adesina Adeyemi-Doro, ya janye daga takarar tare da goyi bayan ɗan takarar APC, Bola Oyebamiji, gabanin zaɓen 15 ga Agusta.
Zaɓen gwamnan Osun na 15 ga Agusta ya ƙara jawo fargabar rikici, yayin da APC da Accord Party suka ce sun rasa mambobi 18 a lokacin shirye-shiryen zaɓen.
Lauya ya ce Oluwo na Iwo ba shi da ikon hana Atiku Abubakar, Peter Obi da sauran ’yan takarar shugaban ƙasa yin yakin neman zaɓe a Osun gabanin zaɓen 2027.
An harbi yaro mai shekaru 12 yayin gangamin jam'iyyar APC a Ilesa, Osun, inda ’yan sanda suka kama Kwamishinan Muhalli domin bincike kan lamarin.
Zaben jihohi
Samu kari