2027: Tsofaffin Gwamnoni 12 da Suka Samu Tikitin Takarar Sanata a APC
Tsofaffin gwamnoni 12 daga jihohi daban-daban sun samu tikitin takarar Sanata a jam’iyyar APC yayin da jam'iyyar ke shirin tunkarar babban zabe mai zuwa.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Nigeria - Wasu daga cikin tsofaffin gwamnonin kasar nan da suka samu tikitin takara zuwa majalisar dattawa sun samu damar ba tare da hamayya ba, yayin da wasu suka doke abokansu a zaben futar da gwani.
Rahotanni sun tabbatar da cewa sanarwa daga jam’iyyar APC ta nuna cewa akalla tsofaffin gwamnoni 11 ta tabbata za su nemi kujera a majalisar dattawa.

Source: Facebook
Legit ta tattaro wasu daga cikin tsofaffin gwamnonin da suka samu wannan dama, wanda wasu daga cikinsu a yanzu haka suna zauren majalisar suna neman tazarce ne.

Kara karanta wannan
Galadima: Mutum 1 da ya samu takara a APC cikin mukarraban Tinubu 7 da suka yi murabus
Akwai wadanda wannan ne karon farkonsu na zuwa majalisar, wasu kuma sun taba zama sanatoci amma suka rasa kujerar, yanzu suke burin sake komawa Abuja.
Tsofaffin gwamnoni 12 sun samu takara a APC
Daga cikin tsofaffin gwamnonin da suka samu damar neman koma wa majalisa akwai wadanda suka taba shiga zauren majalisa, amma daga baya ba su samu sa'ar koma wa ba.
Wasu daga cikinsu kuma manyan kusoshi ne a majalisar dattawa da suke kokarin sake wakiltar mutanen yankunan da suka fito.
Daga cikinsu akwai:
1. Godswill Akpabio
Arise News ta ruwaito cewa tsohon gwamnan jihar Akwa Ibom kuma shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya samu tikitin takarar Sanatan Akwa Ibom North-West bayan zaɓen fitar da gwani na APC da aka gudanar a jihar.

Source: Facebook
Majiyoyi sun ce Akpabio ya samu nasarar ne bayan samun goyon bayan jiga-jigan jam'iyyar APC a jihar ba tare da wata hamayya ba.
2. Malam Ibrahim Shekarau
A ruwayar jaridar Premium Times, tsohon gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau, ya samu tikitin takarar Sanatan Kano ta Tsakiya bayan dawowarsa APC da kuma cimma matsaya da shugabannin jam’iyyar a jihar.

Kara karanta wannan
Jerin gwamnoni 7 da suka samu tikitin takarar sanata na jam'iyyar APC a zaben 2027

Source: Facebook
Wannan na zuwa ne bayan gwamna Abba Kabir Yusuf ya zauna da sauran 'yan takara, aka lallaba su a wani zama a Abuja, har suka janye wa Shekarau.
Shekarau ya taba wakiltar Kano ta tsakiya a majalisa a inuwar APC tsakanin 2019 da 2023.
3. Aliyu Magatakarda Wamakko
A cewar rahoton Vanguard, Sanata Aliyu Wamakko, tsohon gwamnan jihar Sakkwato, ya sake samun tikitin takarar Sanatan Sakkwato ta Arewa domin ci gaba da wakiltar mazabarsa a majalisar dattawa.

Source: Facebook
Shi ma ya samu nasarar ba tare da hamayya ba bayan wakilan kananan hukumomi takwas na yankinsa sun amince ya nemi ragamar jagorantarsu.
Tun 2015 tsohon gwamnan na Sokoto yake majalisa, yana neman wa'adinsa na uku karkashin APC.
4. Mukhtar Ramalan Yero
Rahoton jaridar Punch ya bayyana cewa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mukhtar Ramalam Yero, ya lashe zaɓen fitar da gwani na jam’iyyar APC domin neman kujerar Sanatan Kaduna ta Arewa.

Kara karanta wannan
Bayan 'yan ta'adda sun kutsa makaranta an sace dalibai, gwamna Zulum ya dauki mataki
Ya doke sauran ‘yan takara biyu a zaɓen da aka gudanar a Zariya ranar Litinin 18 ga watan Mayu, 2026, inda ya samu tikitin jam’iyyar APC gabanin babban zaɓe mai zuwa.

Source: Facebook
Da yake bayyana sakamakon zaɓen, jami’in tattara sakamako, Hassan Saleh, ya ce Ramalan Yero ya samu ƙuri’a 6,060, inda ya kayar da Muhammad Mu’azu Mukaddas wanda ya samu ƙuri’u 1,044, yayin da Yusuf Bala Ikara ya samu ƙuri’u 372.
5. Yahaya Bello
Daily Trust ta wallafa cewa tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya lashe zaɓen fitar a gwani na jam’iyyar APC domin neman kujerar Sanatan Kogi ta Tsakiya.
Jami’in da ya jagoranci zaɓen, Dakta Sadiq Mohammed, ne ya sanar da sakamakon a ranar Litinin, 18 ga watan Mayu, 2026 da ya bayyana cewa tsohon gwamnan ya samu jimillar ƙuri’a 72,349.

Source: Facebook
Ya doke manyan abokan takararsa biyu, Ibrahim Yakubu Adoke wanda ya samu ƙuri’u 315, da kuma Momoh Yusuf Obaro wanda ya samu ƙuri’u 188.
6. Adamu Aliero
Daily Post ta kawo rahoton cewa APC ta tabbatar tsohon gwamna Adamu Aliero a matsayin ɗan takarar jam’iyyar APC na kujerar Sanatan Kebbi ta Tsakiya.

Source: Facebook
An cimma wannan bayan dukkanin masu neman tikitin sanatan Kebbi ta Tsakiya sun janye daga takarar, lamarin da ya bai wa Aliero damar zama ɗan takarar bai ɗaya na jam’iyyar.
7. Abubakar Sani Bello
Blueprint ta ruwaito cewa tsohon Gwamnan jihar Neja, Sanata Abubakar Sani Bello, ya samu tikitin takarar sanatan Neja ta Arewa a jam'iyyar APC ta hanyar masalaha.

Source: Facebook
Mai magana da yawun jam’iyyar APC na jihar Neja, Musa Sarkinkaji, ne ya bayyana hakan a Minna ranar Litinin 18 ga watan Mayu yayin da yake ganawa da ‘yan jarida kan yadda aka gudanar da zaɓen fitar da gwani a jihar.
8. Gabriel Suswam
Tsohon gwamnan jihar Binuwai, Gabriel Suswam, ya lashe zaɓen fitar da gwani na kujerar Sanata na yankin Benue ta Arewa maso Gabas a jam’iyyar APC, inda ya kayar da mai ci, Sanata Emmanuel Udende.

Source: Twitter
A cewar sakamakon da jam’iyyar APC ta fitar a hukumance, Suswam, wanda ya rike kujerar sanatan yankin daga 2019 zuwa 2023, ya samu ƙuri’u 131,083 inda ya doke abokan takararsa.
9. Simon Lalong
Channels TV ta ruwaito cewa Simon Lalong, tsohon gwamnan Filato shi ma ya samu tikitin takarar Sanatan Plateau Kudu bayan samun goyon bayan shugabannin APC a jihar.

Source: Facebook
Stella Okotete da ke shugabantar kwamitin zaɓen fitar da gwani na Majalisar Tarayya na jam’iyyar a jihar ce ta sanar da hakan a watan Mayu, 2026.
10. Orji Uzor Kalu
The Sun Nigeria ta kawo labarin cewa sohon gwamnan jihar Abia, Orji Uzor Kalu, ya sake samun tikitin takarar Sanatan Abia ta Arewa domin neman komawa majalisar dattawa.

Source: Facebook
Sanata Kalu ya samu ƙuri’a 65,651, ya doke Nto da ya samu ƙuri’u 2,103, lamarin da ya bai wa shi nasara da tazarar ƙuri’a 63,548.
11. Adams Oshiomhole
Jaridar Independent ta ruwaito cewa Sanata Adams Oshiomhole ya lashe zaɓen fitar da gwani ba tare da hamayya ba a matsayin ɗan takarar jam’iyyar APC na kujerar Sanatan Edo ta Arewa a zaɓen 2027.

Source: Twitter
Oshiomhole wanda ya ci zabe a 2023 shi ne kaɗai ɗan takara a zaɓen, kamar yadda Kassim Otono, wanda shi ne tattara sakamakon zaben fitar da gwanin ya tabbatar.
12. Ifeanyi Okowa
TVC News ta wallafa cewa tsohon gwamnan Delta, Ifeanyi Okowa, wanda ya sauya sheƙa zuwa APC, ya samu tikitin takarar Sanatan Delta ta Arewa a jihar.
Rahotanni sun ce Sanata Okowa ya doke sanatan da ke kan kujerar, Ned Nwoko, da kuma Maryam Ali a zaɓen fitar da gwani na jam’iyyar da aka gudanar a kananan hukumomi tara na shiyyar.

Source: Twitter
A yayin sanar da sakamakon, jami’in zaɓe na APC, Johnbull Tonukari, ya ayyana Okowa a matsayin wanda ya yi nasara bayan ya samu ƙuri’u 113,309, zai nemi ya koma majalisa a badi.
Bola Tinubu zai yi wa APC takara
A baya, mun wallafa cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya lashe jihohi 19 da aka sanar da sakamakonsu a zaben fitar da gwani na shugaban kasa na jam'iyya mai mulki na APC gabanin zabe mai zuwa.

Kara karanta wannan
Tinubu ya fadi tukwicin da zai saka wa 'yan Najeriya da shi idan ya koma Aso Villa
Rahotanni daga jihar Borno sun nuna cewa Tinubu ya samu 100% na kuri’un mambobin jam’iyyar APC da aka kada, lamarin da Tinubu ya bayyana a matsayin nasarar dimokuradiyya ta cikin gida.
Sakamakon da aka tattara daga jihohi daban-daban ya nuna cewa shugaban ya samu gagarumar nasara yayin da ake ci gaba da tattara sauran sakamako daga fadin kasar nan.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


