'Yan Arewa Za Su Amfana da Amurka Ta Kawo Tallafi Mai Kyau a Fannoni 3 a Najeriya

'Yan Arewa Za Su Amfana da Amurka Ta Kawo Tallafi Mai Kyau a Fannoni 3 a Najeriya

  • Rahotanni sun nuna cewa ƙasar Amurka na ci gaba da tallafawa Najeriya wajen bunkasa ababen more rayuwa da harkokin makamashi
  • Hukumar Kasuwanci da Raya Kasa ta Amurka (USTDA) na tallafawa kasashe da dama ciki har da Najeriya a fannoni daban-daban
  • Najeriya na daga cikin kasashen da tsarin ya fara bayyana, musamman a bangarori uku, makamashi, sadarwar zamani da kiwon lafiya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

America - Amurka na neman fadada kasuwancinta, samar da ayyukan yi, karfafa tasirinta a duniya da kuma tabbatar da amfani da amintattun fasahohi a manyan ayyukan raya kasa.

A bangare guda kuma, Najeriya na bukatar ingantaccen makamashi, karfafa tsarin sadarwar zamani, samar da ayyukan yi da kuma aiwatar da manyan ayyukan raya kasa da za su bunkasa tattalin arziki tare da tabbatar da zaman lafiya.

Kara karanta wannan

Turawa sun shiga tashin hankali, mutane 10000 sun mutu a cikin kwana 30 kacal

Tinubu da Trump.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da takwaransa na kasar Amurka, Donald Trump Hoto: @OfficialABAT, @RealDonaldTrump
Source: Getty Images

Premium Times ta ce wannan haduwar muradun kasashen biyu ne suka sa sababbin matakan da Hukumar Kasuwanci da Raya Kasa ta Amurka (USTDA) ke dauka suka zama abin lura.

USTDA ba tallafi kawai take bayarwa ba

A ranar 9 ga watan Yuli, yayin wani taron Washington RoundTable, babban jami'in USTDA, Thomas Hardy, ya bayyana cewa manufar tallafin da hukumar ke bayarwa ita ce taimaka wa ƙawayen Amurka da bunkasa muradun tattalin arziki da tsaro.

A cewarsa, hukumar na taimakawa wajen tsara manyan ayyukan raya kasa tun daga farko domin tabbatar da irin ayyukan da za a gina, kamfanonin da za su aiwatar da su da kuma ka'idojin da za su jagorance su.

Najeriya na daga cikin kasashen da wannan tsari ya fara bayyana karara, musamman a bangarori uku da suka hada da makamashi, sadarwar zamani da kiwon lafiya.

Arewa za ta amfana da tsarin Powergas

Daya daga cikin manyan ayyukan da USTDA ta tallafa shi ne aikin Powergas, wanda ya shafi gina karamin tashar adana iskar gas (LNG) domin karfafa iskar gas a Arewacin Najeriya.

Kara karanta wannan

Fadar shugaban kasa da Gwamna Makinde sun samu sabani kan ceto dalibai a Oyo

A cewar USTDA, aikin zai taimaka wajen rage matsalar makamashi tare da bai wa kamfanonin Amurka damar samar da ingantattun fasahohi.

Thomas Hardy ya bayyana cewa ingantaccen samar da makamashi a Arewacin Najeriya zai taimaka wajen karfafa tsaro a fadin kasar, kamar yadda Tribune Nigeria ta kawo.

Ana kara karfafa sadarwar zamani

Hukumar USTDA ta kuma tallafa wa binciken aikin kebul na karkashin teku mai suna Medusa, wanda ake sa ran zai kara karfin sadarwa a gabar tekun Atlantika ta Afirka.

Ana sa ran aikin zai inganta ingancin intanet, karfafa tsaron bayanai da rage barazanar hare-haren yanar gizo.

Shugaba Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu zaune a wurin taro a Abuja Hoto: @OfficialABAT
Source: Twitter

Ga Najeriya, wannan na nufin samun ingantaccen tsarin sadarwar zamani, yayin da Amurka ke tabbatar da amfani da fasahohinta da ka'idojinta.

Hukumar ta kuma taka rawa wajen samar da cibiyar kula da masu cutar daji a Asibitin Koyarwa na Legas.

Najeriya ta saba wa ikirarin Amurka

A wani labarin, kun ji cewa dakarun sojojin Najeriya sun saba wa ikirarin Amurka cewa ta kwace wasu muhimman kayayyaki daga ‘yan ta’adda.

Kara karanta wannan

PFIPC: Kamfanin Amurka ya kawo ɗauki ga shugaban hukumar bogi da ake ta surutu a Najeriya

Daraktan Yaɗa Labarai na Hedikwatar Tsaro, Birgediya Janar Samaila Uba, ya shaida cewa ba Amurka ce ta ƙwace na'urorin daga hannun ‘yan ta’adda ba.

A cewarsa, gwamnatin Najeriya ce ta miƙa waɗannan kayayyaki ga Amurka a matsayin wani ɓangare na haɗin gwiwar yaƙi da ta’addanci tsakanin ƙasashen biyu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262