'Ya'yan Tsofaffin Shugaban Kasa da Gwamnoni da Suka Samu Takarar Majalisar Wakilai a APC
Abuja, Nigeria - A ranar Asabar, 16 ga watan Mayu, 2026 ne jam’iyya APC mai mulki ta gudanar da zabukan fitar da gwani na yan Majalisar wakilan tarayya a jihohi 36 na Najeriya.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
APC ta gudanar da zabukan fitar gwani kai tsaye wanda aka fi sani da kato bayan kato, bayan yunkurin cimma matsaya kan ‘yan takara ta maslaha ya ci tura a galibin kujerun siyasa.

Source: Facebook
Jam'iyyar APC ta gudanar da zabukan tsaida gwani
Sakamakon rikicin da ya biyo bayan bin tsarin masalaha, APC ta yanke shawarar shirya zabukan domin tsaida yan takararta na zaben 2027, kamar yadda jaridar Punch ta kawo.
Duk da an samu rikici a wasu jihohin yayin gudanar da zaben fitar da gwani, rahotanni sun nuna cewa kwamitocin da APC ta shirya a mazabun yan Majalisar wakilai sun sanar da wadanda suka samu nasara.

Kara karanta wannan
2027: Tsohon gwamnan Ebonyi zai jagoranci kwamitin tantance masu neman takara a NDC
A sakamakon da aka sanar, an ga ‘ya’yan tsofaffin shugabannnin kasa da tsofaffin gwamnoni sun samu nasara a wasu mazabu, lamarin da ya ba su damar lashe tikitin takarar kujerar majalisar tarayya.
APC ta ba 'ya'yan tsofaffin shugabanni takara
Legit Hausa ta gano vewa zuwa yanzu, ‘ya’yan tsofaffin shugabannin kasa biyu da wasu tsofaffin gwamnoni sun samu tikitin takarar APC a zabukan da aka gudanar ranar Asabar, 16 ga Mayu, 2026. Ga su kamar haka.
1. Yusuf Buhari
Yusuf Buhari, dan marigayi tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya zama dan takarar APC a mazabar Sandamu/Daura/Mai’adua ta tarayya a zaben Majalisar Wakilai na 2027.
Muhammadu Buhari ya kasance daya daga cikin fitattun shugabannin Najeriya, inda ya mulki kasar a matsayin shugaban mulkin soja da kuma shugaban kasa na farar hula.

Source: Facebook
Ya rasu a tsakiyar shekarar 2025, sannan aka birne shi a garinsu na Daura. Rasuwarsa ta jawo alhini sosai a fadin kasar, har ma aka ayyana ranar hutun kasa domin jana’izarsa.
Yusuf ya shiga siyasa a hukumance bayan bayyana aniyarsa ta neman kujerar majalisar wakilai a inuwar APC, inda ya samu nasara a zaben da aka gudanar a jihar Katsina.
2. Olumide Osoba
Olumide Osoba, 'dan tsohon gwamnan jihar Ogun, Olusegun Osoba, ya samu tikitin APC na takarar 'dan Majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Abeokuta North/Obafemi Owoy'de/Odeda.
An fara zaben 'dan tsohon gwamnan a wannan kujera ne a shekarar 2011, sannan aka sake zabensa a 2019 da 2023.

Source: Facebook
Dan majalisar ya samu nasara ne ba tare da hamayya ba a zaben fitar da gwani da aka gudanar a fadin mazabar ranar Asabar da ta gabata, kamar yadda Daily Trust ta kawo.
Idan ya yi nasara a zaben 2027, zai zama karo na hudu da Olumide Osoba zai wakilci mazabar a Majalisar Wakilai.
3. Erhiatake Ibori-Suenu
Erhiatake Ibori-Suenu, diyar tsohon gwamnan jihar Delta, ta samu tikitin APC domin wakiltar mazabar Ethiope ta tarayya a zaben Majalisar Tarayya na 2027.
A yanzu haka tana wa’adinta na farko a Majalisar Wakilai, kuma zaben 2027 zai zama wa'adinta na biyu idan ta samu nasara.

Source: Facebook
Yar Majalisar ta tabbatar da nasarar da ta samu a zaben fitar da gwanin APC a wani sako da ta wallafa a shafinta na Facebook.
Ta ce:
"Ina godiya ga mutanen mazabar Ethiope ta Gabas da ta Yamma, wannan nasara ba tawa ce kaɗai ba, tamu ce baki ɗaya. Yanzu ne lokacin da za mu haɗu wuri guda cikin haɗin kai da manufa ɗaya.
4. Chinedum Orji
Chinedum Orji, 'dan tsohon gwamnan jihar Abia, Theodore Orji, na daga cikin ‘ya’yan tsofaffin gwamnoni da suka samu tikitin APC a zabukan fitar sa gwani na ranar Asabar.
An zabe shi a matsayin dan takarar APC a mazabar Ikwuano/Umuahia ta tarayya a zaben yan Majalisar Wakilai mai zuwa a 2027.
Jaridar The Sun ta ruwaito cewa APC ta tabbatar da tsohon kakakin majalisar dokokin jihar Abia, Hon Chinedum Orji, a matsayin wanda ya samu nasara a zaben fitar da gwani.

Kara karanta wannan
Zaben Fitar da Gwani: Manyan 'yan majalisa na APC da suka gaza samun tikitin komawa

Source: Facebook
Sanata Danjuma Goje ya rasa tikitin APC
A wani labarin, kun ji cewa tsohon gwamnan Gombe, Danjuma Goje ya rasa tikitin jam'iyyar APC na tsayawa takarar Sanatan Gombe ta Tsakiya karo na biyar a zaben 2027.
DCP Muhammed Ahmed mai ritaya, wanda gwamna Inuwa Yahaya ke goyon baya ne ya samu nasara a zaben fitar da gwanin da aka gudanar ranar Litinin.
Tun da farko dai an zabi Ahmed a matsayin dan takarar masalaha na APC a mazabar Sanatan Gombe ta Tsakiya, amma Danjuma Goje ya nuna bai yarda ba.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

