Atiku ko Amaechi?: ADC Ta Sanya Ranar da Za Ta Tsayar da Ɗan Takarar Shugaban Kasa

Atiku ko Amaechi?: ADC Ta Sanya Ranar da Za Ta Tsayar da Ɗan Takarar Shugaban Kasa

  • Kwamitin tantance ‘yan takarar shugaban kasa na jam'iyyar ADC ya tantance Atiku Abubakar, Rotimi Amaechi da Muhammed Hayatu-Deen
  • Ana ci gaba da tattaunawa domin cimma matsaya tsakanin ‘yan takarar kafin zaben fitar da gwani na jam'iyyar da za a yi ranar 25 ga Mayu
  • Amaechi da Atiku sun nuna amincewa da tsarin sulhu idan aka gudanar da shi cikin gaskiya da adalci yayin da Hayatu-Deen ya yi martani

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Abuja - Kwamitin tantance ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC ya tantance tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar a Abuja.

Hakazalika, kwamitin ya tantance tsohon gwamnan Ribas, Rotimi Amaechi da kuma babban masanin tattalin arziki, Muhammed Hayatu-Deen.

ADC za ta ayyana dan takarar shugaban kasa a ranar 25 ga Mayun 2026
Rotimi Amaechi (hagu), da Muhammed Hayatu-Deen (tsakiya) da Atiku Abubakar (dama) a ofishin ADC Abuja. Hoto: @Mohayatudeen, @ChibuikeAmaechi, @atiku
Source: Twitter

ADC na son fitar da dan takara ta sulhu

An gudanar da tantancewar ne a otel din Transcorp Hilton a ranar Laraba, yayin da ake shirin zaben fitar da gwani na shugaban kasa a ranar 25 ga Mayu, in ji rahoton Punch.

Kara karanta wannan

ADC: Atiku ya gurfana gaban kwamitin tantancewa, ya gabatar da muhimman manufofinsa

Rahotanni sun nuna cewa shugabannin jam’iyyar na ci gaba da tuntubar ‘yan takarar domin cimma matsayar sulhu kafin ranar zaben.

Majiyoyi sun bayyana cewa shugabannin ADC na son kauce wa kashe kudade da wahalhalun gudanar da zaben kato bayan kato.

Da aka tuntubi sakataren yada labaran jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya ce har yanzu ba a yanke hukunci kan tsarin da za a bi wajen fitar da dan takara ba.

Ya ce:

“Har yanzu ba a yanke hukunci ba.”

Sai dai wata majiya daga jam’iyyar ta bayyana cewa ana tattaunawa da ‘yan takarar domin a samu mafita cikin lumana.

Majiyar ta ce:

“Shugabannin jam’iyyar na tattaunawa tsakaninsu tare da ganawa da masu neman takara domin a warware batun cikin gaggawa.”

Ta kara da cewa idan ba a cimma matsaya ba, jam’iyyar za ta gudanar da zaben kato bayan kato.

Amaechi da Atiku sun yi magana

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, bayan tantancewar, Rotimi Amaechi ya ce zai amince da tsarin sulhu muddin an gudanar da shi cikin gaskiya da adalci.

Kara karanta wannan

Atiku Abubakar da gaske yake neman takarar shugaban kasa a zaben 2027

Ya ce:

“Ni dan jam’iyya ne. Idan hakan ne matsayar jam’iyya kuma kowa ya shiga tsarin, babu matsala.”

Shi ma Atiku Abubakar ya taba bayyana cewa ADC za ta fara kokarin sulhu kafin ta koma zaben kato bayan kato idan hakan bai yiwu ba.

Atiku ya kuma bayyana cewa zaben 2027 zai zama karo na karshe da zai nemi shugabancin Najeriya, sannan zai amince da d'an takarar da jam'iyya ta tsayar.

Rahoto ya nuna cewa ADC na son yin amfani da sulhu don tsayar da d'an takarar shugaban kasa.
Rotimi Amaechi da David Mark a taron jam'iyyar ADC a Abuja. Hoto: @ADCVanguard_/X
Source: Twitter

Hayatu-Deen ya yi alkawari

Muhammed Hayatu-Deen ya bayyana ADC a matsayin jam’iyyar da ta fi dacewa wajen kayar da APC tare da kawo mafita ga matsalolin Najeriya.

Ya ce ‘yan Najeriya sun fi bukatar shugabanci mai kawo mafita kan tsadar rayuwa, rashin tsaro da rashin aikin yi.

“Mutane na bukatar shugabanci mai tafiya da gaskiya da dabarun farfado da tattalin arziki da dawo da fata ga jama’a.”

- Muhammed Hayatu-Deen.

An hana ADC tsayar da 'dan takara?

A wani labari, mun ruwaito cewa, ADC ta musanta rahotannin da ake yadawa cewa ba za ta samu damar tsayar da 'yan takara ba a babban zaben 2027.

Kara karanta wannan

"Ban nemi zama mataimakin Atiku ba": An fusata Rotimi Ameachi da tambayar tikitin ADC

Mai magana da yawun ADC na kasa, Bolaji Abdullahi ya ce wadannan labarai ba su da tushe, an kirkire su ne domin haifar da rudani.

Jam’iyyar ta kara da cewa tana ci gaba da gina kanta a matsayin babbar jam’iyyar adawa, tare da mai da hankali kan tattara goyon bayan ‘yan Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com