Rikici Ya Barke a Zaben Fitar da Gwani na APC, An Tarwatsa Masu Kada Kuri'a

Rikici Ya Barke a Zaben Fitar da Gwani na APC, An Tarwatsa Masu Kada Kuri'a

  • Rikici ya barke yayin zaben fitar da gwani na jam’iyyar APC a Legas kafin fara kada kuri’a domin zaben tikitin majalisar tarayya
  • Magoya bayan wasu ‘yan takara ne suka tayar da tarzoma tare da tilasta masu kada kuri'a guduwa domin tsira da rayukansu
  • Mambobin jam’iyyar sun bukaci shugabanni da jami’an tsaro su tabbatar da zaman lafiya da gudanar da sahihin zabe a yankin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Legas - Rikici ya barke ranar Asabar yayin gudanar da zaben fitar da gwani na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a karamar hukumar Mushin da ke jihar Legas.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne kafin a fara kada kuri’ar zaben fidda gwani na kujerar majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar Mushin Constituency II.

Rikici ya barke a jam'iyyar APC yayin da ake zaben fitar da gwani a Legas.
Magoya bayan APC suna daga tutar jam'iyyar a wajen wani taro. Hoto: @OfficialAPCNg
Source: Twitter

Mutane sun tsere daga wajen taro

Kara karanta wannan

An kama dattijo da ya shiga asibitin Funtua da niyyar satar mahaifar sabon jariri

Wakilin kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) da ke wurin taron ya ce an shiga rudani ne bayan samun sabani tsakanin magoya bayan wasu daga cikin ‘yan takarar.

Rikicin ya haddasa turmutsitsi yayin da wakilai da magoya bayan jam’iyyar suka rika guduwa domin neman tsira.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ba a fara gudanar da zaben ba yayin da hankula suka ci gaba da tashi a wajen taron.

Manyan ‘yan takara a zaben

Daga cikin fitattun ‘yan takarar da ke neman tikitin jam’iyyar akwai Hon. Seye Oladejo da kuma dan majalisa mai ci, Hon. Oluwatoyin Fayinka, wanda ke neman sake komawa kujerarsa.

Sauran ‘yan takara ma sun halarci zaben fidda gwanin domin neman wakiltar jam’iyyar APC a babban zaben shekarar 2027.

An bukaci a tabbatar da zaman lafiya

Wasu daga cikin wadanda suka halarci taron sun nuna damuwa kan rikicin tare da kira ga shugabannin jam’iyyar da jami’an tsaro su tabbatar da zaman lafiya da gudanar da sahihin zabe.

Sun ce wajibi ne jam’iyyar ta tabbatar da adalci da gaskiya domin kaucewa rikice-rikice yayin shirye-shiryen babban zaben kasa mai zuwa.

Kara karanta wannan

Sulhu ko kato bayan kato: Jam'iyyar APC ta kaddamar da fara zaben fitar da gwani

Jam’iyya ba ta yi magana ba

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, jami’an APC ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba dangane da abin da ya faru.

Jam’iyyar APC na gudanar da zabukan fidda gwani a sassa daban-daban na Najeriya domin tantance ‘yan takarar da za su tsaya mata takara a babban zaben shekarar 2027.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com