Tsohon gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekaru ya yi murabus daga jam'iyyar adawa ta PDP, kuma ana hasashen zai yi birki ne a jam'iyyar APC mai mulki.
Tsohon gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekaru ya yi murabus daga jam'iyyar adawa ta PDP, kuma ana hasashen zai yi birki ne a jam'iyyar APC mai mulki.
Babban bankin Najeriya ya sanar da cewa daga 1 ga Mayun 2026 sababbin dokokin da suka shafi amfani da BVN a su fara aiki. Dokokin BVN 10 za su fara aiki a Najeriya.
Mazauna yankin 'Command' a karamar hukumar Alimosho ta jihar Legas sun yi cirko-cirko yayin da ambaliyar ruwa ta mamaye babbar gadar yankin a ranar Talata.
Wasu tsagerun mahara da ake kyautata zaton fulani makiyaya ne sun halaka rayukan mutane 10 a wasu hare-hare da suka kai lokaci guda a kauyuka 5 a jihar Benue.
Sanata Sani Musa ya soki afuwar da aka yi wa manyan wajen biyan haraji. A shekaru biyar da suka wuce, kusan N17tr aka rasa a kasar nan a dalilin afuwar haraji.
Wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan titin Legas-Abeokuta ya yi sanadiyyar salwantar da rayukan mutum tara. Wasu mutane da dama sun jikkata.
Gwamnatin tarayya ta ce ta gano hanyoyi 32 da ake safarar kayan abinci daga Najeriya zuwa wasu kasashen ba bisa ka'ida ba, wanda hakan ke haifar da tsadar abinci.
Dakarun sojojin saman Najeriya da aka girke a Durbunde da ke karamar hukumar Takai a jihar Kano sun kama wani babban mai garkuwa da mutane mai suna Isah Abdul.
Gwamnatin tarayya da masu sarrafa siminti a Najeriya sun cimma muhimman yarjeniyoyi guda shida bayan sun yi ganawar sirri a birnin tarayya Abuja.
Hukumar yaki da rashawa (EFCC) ta kai sumame ofishin wasu 'yan canjin kudi a Abuja, sun yi awon gaba da mutane 50 da ake zargin suna tsawwala farashin dala.
Wata kungiya a Kano mai suna Inuwar Masarautar Bichi ta sake tura wasika zuwa ga Majalisar jihar kan sake fasalin masarautun da ake tababa a kansu.
Labarai
Samu kari