Aisha Musa
9376 articles published since 09 Agu 2016
9376 articles published since 09 Agu 2016
Gwamna Kashim Shettima na jihar Borno ya yi godiya ga mutanen jihar akan irin biyayya da goyon baya da suka basa cikin shekaru bakwai da suka gabata. Gwamnan yayi alkawarin cewa ba zai sanya baki a zaben fid da gwani na gwamna ba.
Shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Mista Adams Oshiomhole ya gana da mambobi da shugabannin jam'iyyar daga yankin Edo ta Arewa domin bikin babban Sallah da kuma tattaunawa kan lamuran siyasa a yankin.
A rahotanni da aka tattara, an gano cewa wannan ya kasance daya daga cikin ayyuka masu muhimmanci da shugaban kasa Buhari ya fara gudanarwa bayan dawowar shi Abuja daga hutun kwanaki 10 da yayi a birnin Landon.
A yau Litinin, 20 ga watan Agusta ne Musulmai fiye da miliyan biyu daga sassa daban-daban na duniya ke hawan Arfa, inda za su shafe ranar suna gudanar da ibada da neman gafara ga Allah (SWT). Wadanda suke da iko suna hawa dutse.
Shugaban kwamitin sojin ruwa na majalisar dattawa, Sanata Isah Misau, da takwaransa na kwamitin bankuna da kudi, Sanata Rafiu Ibrahim sun shawarci jam’iyyar APC da shugabanninta da su janye daga neman tozarta Saraki.
Yan kwanaki kafin bikin babban Sallah, kakakin majalisar dokokin jihar Oyo, Olagunju Ojo ya bukaci Musulmai a fadin kasar, musamman mahajattan Najeriya dake kasa mai tsariki da suyi addu’an samun nasara ga zaben 2019.
Tsohon mukaddashin shugaban jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Alhaji Abubakar Kawu Baraje, yace a shirye yake ya taka rawar gani domin tabbatar da kudirin shugabancin shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki.
Iyalai sune komai na rayuwa kuma Allah ya mallakawa shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki iyali abun sha’awa. Uwargidansa, Toyin ta wallafa kyawawan hotunan iyalansu a shafinta na Instagram don murnar nasarar da suka samu.
Rahotanni sun kawo cewa wata matashiyar Musulma ‘yar kasar Sweden ta samu nasara a kotu kan wata tuhuma da ake yi mata. Ana dai tuhumarta ne da kin mika hannu ta yi musabaha da wani namiji a lokacin da aka yi mata jarabawar aiki.
Aisha Musa
Samu kari