Zaben 2027: An Fara Hasashen Siyasa bayan Obasanjo Ya Gana da Kwankwaso a Kano
- Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya kai ziyara ta musamman ga Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a jihar Kano
- Kwankwaso tare da dan takarar gwamna na NDC a Kano, Aminu Abdulsalam Gwarzo, sun tarbi Obasanjo yayin da suka gaisa cikin yanayi na mutuntawa
- Mai taimaka wa Kwankwaso kan harkokin yada labarai ya ce an yi tattaunawa mai kyau, amma bai bayyana cikakken abin da shugabannin suka tattauna ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Kano - Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya kai ziyara na musamman ga Rabiu Musa Kwankwaso.
'Dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar NDC ya karbi bakuncin Olusegun Obasanjo a gidansa da ke titin Miller a Kano.

Source: Facebook
Mai taimaka wa Kwankwaso kan harkokin yada labarai, Saifullahi Hassan, ya tabbatar da faruwar ziyarar cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa a Facebook.
Obasanjo ya gana da Kwankwaso a Kano
Kwankwaso tare da dan takarar gwamna na NDC a Kano, Aminu Abdulsalam Gwarzo ne suka tarbi Obasanjo.
Ya bayyana cewa ziyarar ta bai wa shugabannin damar gaisawa da tattaunawa cikin yanayi na sada zumunci, amma bai bayyana cikakken bayanin tattaunawar ba.
Kwankwaso ya taba rike mukamin ministan tsaro a wa’adi na biyu na gwamnatin Obasanjo tsakanin shekarun 2003 zuwa 2007, inda suka yi aiki tare a matakin tarayya.
Tun bayan wannan lokaci ne aka ce dangantaka mai kyau ta ci gaba da kasancewa tsakanin Kwankwaso da Obasanjo, lamarin da ya sa suke ci gaba da mu’amala.
Daga bisani, Saifullah Hassan ya tabbatar a Facebook cewa Obasanjo, Kwankwaso da manyan mutane daga fadin Najeriya sun isa fadar Sarki Muhammadu Sanusi II domin bikin nadin sarauta.
Ya ce:
"Mai Girma Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, PhD, FNSE, ya isa Fadar Mai Martaba Sarkin Kano domin halartar bikin naɗa rawanin Abubakar Balarabe Mahmoud, OON, SAN, a matsayin Garkuwan Kano."

Kara karanta wannan
Kano ta yi zarra, ta fi dukkan jihohin Najeriya sababbin masu rijistar katin zaɓe

Source: Twitter
Alalar da ke tsakanin Obi da Obasanjo
'Dan takarar shugaban kasa na NDC, Peter Obi, shi ma na daga cikin makusantan Obasanjo kuma yana da kyakkyawar alaka da tsohon shugaban kasar.
Obasanjo ya goyi bayan Obi a zaben shekarar 2023, yayin da rahotanni ke cewa ya taka muhimmiyar rawa wajen hada kawancen siyasa tsakanin Obi da Rabiu Kwankwaso domin zaben 2027.
Sai dai sanarwar da ta tabbatar da ziyarar ba ta bayyana ko batun siyasar 2027 ko wasu muhimman al’amuran kasa sun kasance cikin abubuwan da aka tattauna ba.
Ziyarar ta jawo hankalin masu bibiyar harkokin siyasa, musamman saboda matsayi da tasirin da Obasanjo da Kwankwaso ke da shi a siyasar Najeriya.
Kwankwaso ya yi barazana ga Fasto Ayodele
Mun ba ku labarin cewa dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam'iyyar NDC, Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi barazanar shigar da kara kan.

Kara karanta wannan
Zargin bata suna: Fasto Ayodele ya fayyace komai a martani ga barazanar Kwankwaso
Primate Elijah Ayodele Sanata Kwankwaso ya yi barazanar shigar da karar ne kan malamin addinin saboda zargin bata masu suna da kimarsa ta siyasa.
Madugun na Kwankwasiyya ya ce Primate Ayodele ya yi kalamai wadanda suke na cin mutunci ne a gare shi da kuma kimarsa.
Asali: Legit.ng
