Kada ku bari 'yan siyasa su yi amfani da ku - Sarkin Musulmi ga matasa
- Sarkin Musulmi ya ja kunnen matasa akan ‘yan siyasar kasar
- Ya ce kada su bari suna amfani da su wajen aikata barna
- Hakan na kunshe ne a sakonsa na babban Sallah
Mai martaba Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Sa’ad ya shawarci matasa da kada su bari 'yan siyasa su yi amfani da su, a lokacin siyasa suna saran junan su, suna shaye shaye alhali 'ya'yansu siyasar ba su gun.
Sarkin ya bayyana hakan ne a jawabin da yake gabatarwa a fadar sa na bikin sallah babba.
![Kada ku bari 'yan siyasa su yi amfani da ku - Sarkin Musulmi ga matasa Kada ku bari 'yan siyasa su yi amfani da ku - Sarkin Musulmi ga matasa](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt3v2q9vmtbhr.jpeg?v=1)
Ya ce "Idan kuna son Buhari, hanyar da za ku tabbatar da nasarar sa ita ce ku karbi katin zabenku, haka shi ma Gwamna Tambuwal da sauran 'Yan takarar".
KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Sojoji sun kai mamaya Ikorodu a kokarinsu na gano yan kungiyar asirin da suka kashe wani soja
Ya kara da cewa "Mu rika yin siyasa kamar yadda ya kamata, mu kaucewa kalaman batanci da rarrabuwar kawuna a cikin siyasa. Sannan kuma bayan zabe duk wanda Allah Ya baiwa nasara mu bashi goyon baya domin ya samu nasara".
A baya Legit.ng ta rahoto cewa kungiyoyin fafutuka a jihar Nasarawa sun nuna damuwarsu kan yawaitar mambobin kungiyar Hakika a jihar da kuma yadda matasa ke shiga kungiyar.
Wani masanin harkar tsaro, Dakta Nwani Aboko, ya laburta wannan abu ne a taron da kungiyar North East Regional Initiative (NERI) ta shirya kan dakile tsatsauran ra’ayi a garin Lafiya, babban birnin jihar Nasarawa.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa
Ko a http://twitter.com/naijcomhausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Asali: Legit.ng