Gwamna Dauda Lawal Ya Amince a Fara Biyan Matasa 'Yan NYSC Alawus a Jihar Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Amince a Fara Biyan Matasa 'Yan NYSC Alawus a Jihar Zamfara

  • Gwamna Dauda Lawal ya amince da biyan alawus ga matasa masu yi wa kasa hidima (NYSC) a jihar Zamfara
  • Gwamnatin jihar Zamfara ta ce hakan na nuna kulawarta ga jin dadin matasan da ke yi wa jihar hidima na kowane rukuni na NYSC
  • Gwamna Lawal ya umurci Ofishin Akanta Janar da ya fara shirye-shiryen aiwatar da biyan kudaden domin walwalar matasan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Zamfara, Nigeria - Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da fara biyan alawus da tallafin kudi ga masu yi wa kasa hidima (NYSC) da ke gudanar da aikin bautar kasa a fadin jihar.

A cewar gwamnatin Zamfara, wannan mataki na nuna irin jajircewar Gwamna Lawal wajen kula da walwala da jin dadin matasan da ke bayar da gudunmawa wajen bunkasa bangarori daban-daban na jihar.

Kara karanta wannan

NASFAT ta ja hankalin musulmai, ta nemi su taimaka kan matsalar tsaron Najeriya

Gwamna Lawal.
Gwamna Dauda Lawal yan rattaba hannu a kan takardar doka a gidan gwamnatin jihar Zamfara Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Vanguard ta rahoto cewa hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labarai da Al’adu na jihar Zamfara, Mahmud Muhammad Dantawasa, ya fitar yau Alhamis, 25 ga watan Yuni, 2026.

Rukunin 'yan NYSC da za su amfana

Sanarwar ta bayyana cewa amincewar ta shafi masu yi wa kasa hidima daga na rukunin A Stream I da II har zuwa rukunin C Stream I da II.

Gwamnatin ta ce ta dauki matakin ne domin nuna godiya ga kishin kasa, sadaukarwa da gudunmawar da mambobin NYSC ke bayarwa a bangarorin ilimi, lafiya, noma da sauran fannonin da ke da muhimmanci ga ci gaban Zamfara.

Gwamna Lawal ya umarci a fara biya

Sanarwar ta kara da cewa Gwamna Lawal ya umurci Ofishin Akanta Janar na jihar da ya dauki dukkan matakan da suka dace domin fara biyan kudaden cikin sauki da bin ka’idojin gwamnati.

“Gwamna Lawal ya bayar da umarni ga Ofishin Akanta Janar da ya yi dukkan shirye-shiryen da suka dace domin aiwatar da wannan shiri na bai wa masu yi wa kasa hidima alawus.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Sakkwato ta yi magana kan rahoton da ake yadawa game da Bello Turji

"Gwamnatin Zamfara na da kudurin tabbatar da cewa an gudanar da tsarin cikin sauki tare da bin dukkan matakan da aka tanada,” in ji sanarwar.
Matasan NYSC.
Matasa masu yi wa kasa hidima a sansanin daukar horo na NYSC Hoto: @OfficialNYSCNg
Source: Twitter

An yaba wa masu yi wa kasa hidima

Gwamnatin Zamfara ta bayyana jin dadinta ga masu yi wa kasa hidima da suka amince su gudanar da aikin bautar kasa a jihar, tare da yabawa da irin gudunmawar da suke bayarwa wajen ci gaban al’umma.

Ta ce za ta ci gaba da daukar matakan da za su inganta walwala da yanayin aiki na matasan da ke yi wa jihar hidima, kamar yadda Punch ta rahoto.

Gwamna Lawal ya kafa tarihi a Zamfara

A wani labarin, kun ji cewa Gwamnan Dauda Lawal ya kafa tarihi da ya gina filin jirgin sama na kasa da kasa, irinsa na farko a tarihin jihar Zamfara.

Rahotanni sun nuna cewa an kaddamar da wannan filin jirgi ne a lokacin jigilar maniyyata zuwa kasa mai tsarki, inda jirgi ya dauki alhazai dag Gusai zuwa Saudiyya.

Gwamnan ya bayyana gina Filin Jirgin Sama na Kasa da Kasa a brinin Gusau a matsayin babban aikin da gwamnatinsa ta aiwatar wanda ya shiga tarihin jihar Zamfara.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262