Mutane 2 sun mutu a hatsarin mota a ranar Sallah

Mutane 2 sun mutu a hatsarin mota a ranar Sallah

Hukumar dake kula tsaron rayuka a hanya (FRSC) a jihar Ogun ta tabbatar da mutuwar mutane biyu a ranar Talata lokacin da wata motar kasuwa ta yi dungure a babban titin Lagas-Ibadan.

Kwamandan hukumar, Mista Clement Oladele ya fadama kamfanin dillancin labaran Najeriya cewa hatsarin ya afku ne da misalin karfe 5:00 na yamma a babban titin Lamona Park.

Mutane 2 sun mutu a hatsarin mota a ranar Sallah
Mutane 2 sun mutu a hatsarin mota a ranar Sallah

Ya bayyana ewa tayar motare ta fashe wanda yayi sanadiyar da motar ta dunga mirginawa.

KU KARANTA KUMA: Buhari da tsoffin shugabanni sun gazawa yan Najeriya – Dan takarar shugaban kasa

Mutane biyu ne suka rasa ransu a wannan hatsari yayinda wasu da dama suka jikkata, inda aka kwashe su zuwa asibitin Isara, Ogere.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng