Aisha Musa
9376 articles published since 09 Agu 2016
9376 articles published since 09 Agu 2016
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa sun kai mamaya gidan da ýaýan Atiku Abubakar biyu ke zama a Abuja a karshen mako. Haka zalika Chimeka Orji, dan tsohon gwamnan jihar Abia, Theodore Orji na na zama ne a gidan.
Ministan ilimi, Mallam Adamu Adamu, ya bayyana cewa yawan jahilai da ba su iya karatu da rubutu ba a Najeriya sun kai kusan miliyan 60, wato kenan a takaice kashi 1 bisa 3 na daukacin mutanen Najeriya duk jahilai ne.
Magoya bayan Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) sun mayar da martani ga matakin da hadakar jam'iyyun adawa suka zartar na marawa dan takarar babbar jam'iyyar adawa ta kasar wato PDP.
Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, ya bayyana zakka a matsayin wani makami da za’a iya amfani da shi wajen yakar talauci a tsakanin al’umma. Basaraken ya fadi hakan a wajen taron rabon zakka wanda gidauniyar Jaiz ta shirya.
Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal a ranar Alhamis, 6 ga watan Disamba ya caccaki takwaransa na jihar Kaduna, Nasir El-Rufai kan furucin da yayi game da kamfen din jam’iyyar PDP da ya gudana a yankin arewa maso yamma.
Kwamrad Adams Oshiomhole, shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa, ya bayyana cewa sabbin yan takarar gwamna a APC 20 da gwamnoni masu ci guda tara ne za su yi takarar kujerar gwamna a zaben 2019.
Karamin ministan muhalli, Usman Jibrin ya zama sarkin garin Nasarawa na 13, a karamar hukumar Nasarawa da ke jihar Nasarawa. Mista Jibrin ya kasance shugaban ma’aikatar tun bayan barin tsohuwar minister, Amina Mohammed.
An kama masu laifin ne a ranar 30 ga watan Nuwamba ta hanyar rahoton kwararru da hukumar ta samu akan ayyukan damfara da wajen zaman yan damfarana hanyar fili jirgin sama na Abuja, inda suke guanar da rayuwar da tafi karfin su.
An samu tashin hankali a gidan gwamnatin jihar Benue, a Makurdi a ranar Laraba, 5 ga watan Disamba lokacin da wani bangare na ginin ya kama da wuta.An tattaro cewa koda dai ba’a rasa rai ba lamarin a dakatar da ayyuka cak.
Aisha Musa
Samu kari