Rikici Ya Barke a Majalisar Dokokin Neja, An Dakatar da Zama kan Wata Takaddama
- An samu barkewar rikici a majalisar dokokin jihar Neja a zaman majalisar na yau Litinin bayan wani dan majalisa ya gabatar da sabon kuduri
- Rikicin dai ya samo asali ne daga batutuwan da suka shafi alakar majalisa da bangaren zartarwa da kuma zabukan fitar da gwani na APC
- Hayaniya ta barke a zauren majalisar, lamarin da ya tilasta dakatar da zaman bayan mafi yawan ‘yan majalisar sun kada kuri’a kan hakan
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Neja - Wani rikici mai zafi ya barke ba zato ba tsammani a majalisar dokokin jihar Neja a ranar Talata, 23 ga Yunin 2023, lamarin da tilasta aka dakatar da zaman ranar.
Rahoto ya nuna cewa zaman majalisar ya rikide zuwa ce-ce-ku-ce mai zafi kan wasu batutuwan da ‘yan majalisar suka ce har yanzu ba a shawo kansu ba tsakanin majalisa da bangaren zartarwa na gwamnati.

Source: Facebook
Yadda aka fara zaman majalisa a Neja
Akwai rade-radin cewa matsalolin da ake takaddama a kai na da alaka da korafe-korafen da suka biyo bayan zaben fitar da gwani na jam’iyyar APC da aka gudanar kwanan nan, in ji rahoton Tribune.
An fara samun rashin jituwar ne jim kadan bayan bude zaman ranar, lokacin da dan majalisar da ke wakiltar mazabar Chanchaga, Mohammed Abubakar Kabir (Ustaz), ya gabatar da kudurin a dakatar da ayyukan majalisar har sai an warware matsalolin da ake fama da su.
Kabir ya ce tarihi zai yi wa majalisar mummunan hukunci idan ta kyale matsalolin da ake ciki ba tare da magance su ba.
Rikici ya barke a zaman majalisar Neja
Sai dai ba a ba shi damar fadin cikakken bayanin batutuwan a zauren majalisar ba, inda ‘yan majalisar suka amince cewa za a tattauna batun ne a wani taron sirri na shugabannin majalisar.
Lamarin ya kara tsananta ne lokacin da dan majalisar da ke wakiltar Lavun, Jibrin Ndagi Baba, ya kalubalanci kudurin.
Ya dage cewa ya kamata majalisar ta ci gaba da gudanar da ayyukanta saboda ta riga ta dawo daga hutun zaman majalisa, in ji rahoton Daily Post.
Rashin jituwar da aka samu ya haifar da hayaniya a zauren majalisar, lamarin da ya tilasta dakatar da zaman bayan mafi yawan ‘yan majalisar sun kada kuri’ar goyon bayan a dakatar da shi.

Source: Facebook
Shugaban majalisa ya kwantar da hankula
A yayin da ake kokarin kwantar da hankalin ‘yan majalisar, shugaban majalisar dokokin jihar Neja, Abdulmalik Sarkindaji, ya yi kira ga mambobin majalisar su zauna lafiya tare da mutunta ra’ayoyin juna.
Rt. Hon. Abdulmalik Sarkindaji ya bukaci ‘yan majalisar su ci gaba da nuna mutuntaka da fahimtar juna, domin ta hakan ne za su iya gudanar da ayyukan majalisa cikin tsari.
An sako mataimakin shugaban majalisa
A wani labari, mun ruwaito cewa, mataimakin shugaban majalisar dokokin Kebbi, Muhammad Samaila Bagudu ya shaki iskar 'yanci bayan kwashe kwanaki a hannun 'yan bindiga.
Samaila Bagudu ya shiga hannun 'yan bindiga ne lokacin da suka yi awon gaba da shi jim kadan bayan kammala sallar Isha'i.
Rundunar 'yan sandan jihar Kebbi ta tabbatar da kubutar da mataimakin shugaban majalisar dokokin a wata sanarwa da ta fitar.
Asali: Legit.ng


