Nasarorin Buhari ya fi na shekaru 16 da PDP ta yi tana mulki – Omo-Agege

Nasarorin Buhari ya fi na shekaru 16 da PDP ta yi tana mulki – Omo-Agege

- Sanata Ovie Omo-Agege ya bayyana shekaru uku da shugaban kasa Muhammadu Buhari yayi yana mulki a masayin mai cike da nasara idan aka kwatanta da shekaru 16 da jam’iyyar PDP tayi

- Dan majalisan ya bayyana hakan ne a Ughelli, jihar Delta lokacin kaddamar da kungiyar kamfen dinsa na mutum 400 karkashin jagorancin Cif Francis Atanoneyovwin.

- Yace gwamnat ta yi matukar kokari wajen yakar cin hani da rashawa, da kuma yaki da ta’addanci a yankin arewa maso gabashin kasar kuma suna kan nasara a yakin

Sanata mai wakiltan yankin Delta ta tsakiya a majalisar dokokin kasar, Sanata Ovie Omo-Agege ya bayyana shekaru uku da shugaban kasa Muhammadu Buhari yayi yana mulki a masayin mai cike da nasara ga yan Najeriya idan aka kwatanta da shekaru 16 da jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) tayi.

Dan majalisan ya bayyana hakan ne a Ughelli, jihar Delta lokacin kaddamar da kungiyar kamfen dinsa na mutum 400 karkashin jagorancin Cif Francis Atanoneyovwin.

Nasarorin Buhari ya fi na shekaru 16 da PDP ta yi tana mulki – Omo-Agege
Nasarorin Buhari ya fi na shekaru 16 da PDP ta yi tana mulki – Omo-Agege
Asali: Depositphotos

Omo-Agege yayinda yake yaba ma gwamnatin APC yayi bayanin cewa gwamnat ta yi matukar kokari wajen yakar cin hani da rashawa, da kuma yaki da ta’addanci a yankin arewa maso gabashin kasar kuma suna kan nasara a yakin.

KU KARANTA KUMA: 2019: Gwamnonin APC 3 sun yi ganawar sirri da Omisore

Yace: “Ta hanar shirin ci gaba da gwamnatin tayi na N-Power, TradersMoni da ciyar da yaran makaranta, yan Najeriya da dama sun samu aikin yi don haka sun cancanci a sake zabar gwamnatin APC domin ci gaban wannan shirin."

Ya kuma jadadda tarin kokarin da Buhari yayi a jihar Delta ta hanyar gina manyan hanyoyi fiye da na gwamnatocin jiha.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng