Yanzu Yanzu: EFCC ta tsare Doyin Okupe

Yanzu Yanzu: EFCC ta tsare Doyin Okupe

- Hukumar EFCC ta tsare mai ba da shawara ga Darakta Janar na kungiyar kamfen din dan takarar shugaban kasa na PDP akan labarai, Doyin Okupe

- Kakakin jam’iyyar PDP Kola Ologbodiyan ya bayyana hakan a shafin twitter

- Ya ce yanzu lokaci ne na tozarci, cin zarafi da barazana ga mambobin jam’iyyar PDP

Hukumar yaki da cin hanci da hana yiwa tattalin arziki zagon kasa (EFCC) ta tsare hadimin Darakta Janar na kungiyar kamfen din dan takarar shugaban kasa na PDP, Doyin Okupe.

Kakakin jam’iyyar PDP Kola Ologbodiyan ya bayyana cewa yanzu a shiga lokacin ci wa mambobin jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) mutunci da tozarci tare da barazana.

Yanzu Yanzu: EFCC ta tsare Doyin Okupe
Yanzu Yanzu: EFCC ta tsare Doyin Okupe
Asali: Depositphotos

Kola Ologbondiyan ya wallafa a shafin twitter a daren ranar Litinin, 10 ga watan Disamba cewa: “Hukumar yaki da cin hanci da hana yiwa tattalin arziki zagon kasa ta kama hadimin Darakta Janar na kungiyar kamfen din shugaban kasa na PDP, @doyinokupe.

“Yanzu lokaci ne na tozarci, cin zarafi da barazana ga mambobin jam’iyyar PDP”, cewar shi.

KU KARANTA KUMA: Boko Haram na iko da kananan hukumomi 17 a Borno - Sani Zoro

A baya mun ji cewa hukumar yaki da cin hanci da rashawa sun kai mamaya gidan da ýaýan Atiku Abubakar biyu ke zama a Abuja a karshen mako, jaridar Premium Times ta ruwaito.

Haka zalika Chimeka Orji, dan tsohon gwamnan jihar Abia, Theodore Orji na zama ne a gidan. An kuma rahoto cewa jami’an hukumar yaki da rashawan sun binciki sashinsa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng