2019: Gwamnonin 9 masu mulki, da sabbin yan takara 20 ne za su yi takarar gwamna a APC - Oshiomhole

2019: Gwamnonin 9 masu mulki, da sabbin yan takara 20 ne za su yi takarar gwamna a APC - Oshiomhole

Kwamrad Adams Oshiomhole, shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ya bayyana cewa sabbin yan takarar gwamna a APC 20 da gwamnoni masu ci guda tara ne za su yi takarar kujerar gwamna a zaben 2019.

Ya bayyana hakan ne lokacin wani taron tattaunawa da kwamitin jam’iyyar ta yi da yan takarar kujerar gwamna a zaben 2019, shugabannin jihad a kuma sakatarorin jam’iyyar na jihad a kasa a Abuja a ranar Ahamis, 6 ga watan Disamba.

2019: Gwamnonin 9 masu mulki, da sabbin yan takara 20 ne za su yi takarar gwamna a APC - Oshiomhole
2019: Gwamnonin 9 masu mulki, da sabbin yan takara 20 ne za su yi takarar gwamna a APC - Oshiomhole
Asali: UGC

Legit.ng ta tattaro cewa Oshiomhoe ya shawarci yan takarar gwamna akan sukar nasarorin gwamnoni masu barin gado sannan ya shawarce su da kada su yi abunda ya saba ka’ida a lokacin kamfen.

Ya ci gaba da sukar wadanda suke yi ikirarin cewa babu zaben fidda gwani, inda ya bayyana su a matsayin masu adawa da basa neman mafita.

KU KARANTA KUMA: APC ba ta da alkibla don haka na fice na bar ta – Inji Ghali Na’Abba

Ya bukaci shugabannin jam’iyyar a jiha da su yi aiki kai-da-kai da dukkanin yan takarar ta hanyar tabbatar da cewar sun yi nasara a dukkan matakai.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng