2019: Gwamnonin 9 masu mulki, da sabbin yan takara 20 ne za su yi takarar gwamna a APC - Oshiomhole
Kwamrad Adams Oshiomhole, shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ya bayyana cewa sabbin yan takarar gwamna a APC 20 da gwamnoni masu ci guda tara ne za su yi takarar kujerar gwamna a zaben 2019.
Ya bayyana hakan ne lokacin wani taron tattaunawa da kwamitin jam’iyyar ta yi da yan takarar kujerar gwamna a zaben 2019, shugabannin jihad a kuma sakatarorin jam’iyyar na jihad a kasa a Abuja a ranar Ahamis, 6 ga watan Disamba.
Legit.ng ta tattaro cewa Oshiomhoe ya shawarci yan takarar gwamna akan sukar nasarorin gwamnoni masu barin gado sannan ya shawarce su da kada su yi abunda ya saba ka’ida a lokacin kamfen.
Ya ci gaba da sukar wadanda suke yi ikirarin cewa babu zaben fidda gwani, inda ya bayyana su a matsayin masu adawa da basa neman mafita.
KU KARANTA KUMA: APC ba ta da alkibla don haka na fice na bar ta – Inji Ghali Na’Abba
Ya bukaci shugabannin jam’iyyar a jiha da su yi aiki kai-da-kai da dukkanin yan takarar ta hanyar tabbatar da cewar sun yi nasara a dukkan matakai.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT
Asali: Legit.ng