'Ya Kamata Isra'ila Ta Tsaya da Kafarta': Netanyahu kan Taimakon Makamai daga Amurka

'Ya Kamata Isra'ila Ta Tsaya da Kafarta': Netanyahu kan Taimakon Makamai daga Amurka

  • Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya yi magana kan dogaro da kasar ke yi kan Amurka
  • Netanyahu ya ce ya kamata su rage dogaro da makaman Amurka, tare da ƙarfafa masana’antunsu
  • Ya bayyana cewa Isra’ila na ci gaba da fafatawa da Iran da ƙawayenta, yana mai cewa makomar ƙasar za ta dogara ne da ƙarfinta

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Tel Aviv - Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya yabawa Amurka kan gudunmawar da ta ke ba kasar.

Netanyahu ya bayyana cewa ƙasarsa na buƙatar samun ‘yanci daga dogaro da makaman Amurka, tare da bunƙasa masana’antar kera makamai ta cikin gida.

Yayin wata ganawa da jami’an rundunar ajiya a yankin Gush Etzion da ke Yammacin Kogin Jordan, Netanyahu ya ce yana matuƙar godiya ga goyon bayan Amurka, cewar Al Jazeera.

Kara karanta wannan

Ekiti: Zaben gwamna ya zo da zafinsa, an kona ofishin yan sanda kurmus

Netanyahu ya ƙara da cewa dole ne Isra’ila ta rika ƙera makaman da kanta domin tabbatar da tsaron ƙasa da kuma fuskantar barazanar da take gani.

Ya ce:

“Ina matuƙar yaba wa tallafin da muka samu daga abokanmu na Amurka tsawon shekaru.
"Amma yau ina cewa muna buƙatar tsarin kera makamai namu.”

A cewarsa, Isra’ila na fafatawa da Iran da ƙungiyoyin da ke goyon bayanta, kuma ta yi musu mummunar illa, duk da cewa rikicin bai ƙare ba.

Ya ce makomar Isra’ila a shekaru talatin masu zuwa za ta dogara ne da irin ƙarfin da ƙasar ta gina a yau da kuma matakan tsaro.

Firaministan ya bayyana cewa gwamnati na ƙoƙarin gina ƙarin ƙarfi, haɓaka fasahohi, da kuma horar da sababbin shugabannin rundunonin soji masu ƙwarewa.

Ya ce burinsa shi ne Isra’ila ta mallaki cikakkiyar damar kera makamai da kanta domin rage dogaro da tallafin ƙasashen waje.

Netanyahu ya sha alwashin kawo ƙarshen taimakon sojin Amurka ga Isra’ila a cikin shekaru goma masu zuwa, yana mai neman sabuwar hanya.

Kalaman nasa sun zo ne yayin da ake nuna damuwa a Isra’ila kan yiwuwar Amurka ta ƙara takaita wasu matakan soji yayin tattaunawa da Iran.

Kara karanta wannan

Roko na musamman da Sarki Sanusi II ya yi ga kungiyar EU game da Kano

Ya ce:

“Muna buƙatar kuɓuta daga dogaro, mu ci gaba da gina ƙarfi, mu ƙara amfani da fasaha, kuma mu horar da ƙarin shugabanni.”

A makon da ya gabata, Mataimakin Shugaban Amurka, JD Vance, ya ce kusan kashi biyu bisa uku na makaman kariyar da suka taimaka wa Isra’ila sun fito ne daga Amurka.

Jami’an Amurka da Isra’ila sun kuma bayyana cewa ana tattaunawa kan sabon tsarin haɗin gwiwar tsaro na shekaru goma wanda zai mayar da dangantakar zuwa haɗin gwiwa mai anfani ga ɓangarorin biyu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.