Yan Fashi Da Makami
Wasu ’yan bindiga sun kai mamaya kauyen Kawaran Rafi da ke Karamar Hukumar Igabi da ke jihar Kaduna, inda suka kashe babban Limamin garin, wato Dan Liman Isah.
Wata mata mai suna Suwaiba Naziru, da 'yan bindiga suka yi garkuwa da ita a kauyen Biya ki Kwana da ke jihar Katsina ta bayyana yadda ta haihu a hannun su.
Za ku ji labarin wani da ya yi kwana da kwanaki tsare a dajin Birnin Gwari. Mutumin da aka yi garkuwa da shi, ya ce ya ga ana horas da kananan yara a daji.
Wasu yan bindiga da ake zaton masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da wani limamin Katolika na Owerri da ke jihar Imo, Moses Chikwe, tare da direbansa.
Wasu yan fashi da makami sun kai hari garuruwa shida a jihar Katsina, sun yi garkuwa da mutane 50 ciki harda sabbin ma'aurata sannan kuma suka kashe mutum biyu.
Wasu yan bindiga sun kashe Alhaji Ahmodu Mohammed, jigon jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a karamar hukumar Bosso da ke jihar Niger a ranar Alhamis.
A jiya wata Kotu a jihar Ogun ta yankewa mai laifin garkuwa da mutane dauri. ‘Dan shekara 44 din da aka kama da laifin garkuwa da mutane zai tafi gidan kurkuku.
A wani hari da aka kai cikin tsakar dare kwanaki aka sace Dr. Ibrahim G. Bako na ABU Zaria. 'Yanuwan wannan Malami sun tabbatar da cewa an fito da shi jiya.
Za ku ji labarin yadda ‘yan fashi da makami sun kashe wani mai NYSC, Bomoi Suleiman Yusuf. Amma an gano cewa ba a yi garkuwa da ‘Yan NYSC 16 a hanyar Abuja ba.
Yan Fashi Da Makami
Samu kari