Albashin ma'aikata
Bola Tinubu zai sanar da karin albashin Ma’aikata a Ranar 1 ga Mayu. Abin da ake tunani shi ne Tinubu zai sanar da mafi karancin albashin da za a koma amfani da shi
A ranar Laraba ne majalisar wakilai ta amince da sabuwar dokar ƙarin albashi da alawus ga babban joji na ƙasa (CJN) da sauran alƙalan kotunan Najeriya.
Duk da halin matsi da 'yan kasa su ke ciki, Shugaba Tinubu ya bukaci yin gyaran fuska daga Majalisa kan alawus da albashin ma'aikatan shari'a a kasar.
A ranar Talata ne majalisar dokokin jihar Abia ta zartar da kudirin dakatar da biyan kudaden fansho ga tsofaffin gwamnoni da mataimakansu a jihar.
Yayin da 'yan Najeriya ke cikin mawuyacin hali, ashe wasu gwamnoni su na shan wahala bayan Gwamna Charles Soludo ya ce ya shafe shekaru biyu ba tare da albashi ba.
Dangane da karin albashi, kungiyar 'yan fansho ta NUP ta koka kan cewa har yanzu akwai tsofaffin ma'aikata da ake biya N1,500 a wata matsayin kudin fansho.
Bayan janye tallafin man fetur wanda ya haifar da tsadar rayuwa a Najeriya, akwai gwamnonin jihohi 12 da suka yi karin albashi. Legas da Ondo na biyan N35,000.
Gwamnan jihar Neja, Muhammad Umar Bago, ya amince da ƙarin N20,000 a albashin ma'aikatan jiharsa, ya kuma ba da umarnin a fara tura masu nan take.
Za a ji Shugaban kasa, Bola Tinubu ya roki gwamnonin jihohi 36 da su fara biyan kudaden rage radadin cire tallafin mai domin kawo sauki a cikin al'umma.
Albashin ma'aikata
Samu kari