"Jarumar Fina Finan Najeriya Ta Mutu a Ofishin Ƴan Sanda," Saurayinta Ya Yi Zargi
- An ce marigayiyar jarumar Nollywood, Temitope Osoba, ta rasu a wani ofishin ’yan sanda da ke Ikorodu a Legas, sabanin rade-radin cewa ciwon kansar nono ne ya yi sanadin mutuwarta
- Wanda za ta aura, Annabi Itunu Onadeko, ya ce wani mutum da ba a san ko wanene ba ne ya kira shi da tsakar dare ya sanar da shi mutuwar jarumar
- Onadeko ya musanta zargin cewa an saka wa Osoba guba ko kuma an wulakanta ta kafin rasuwarta, tare da cewa ciwon kansa da ta yi fama da shi ba shi ne ya kashe ta ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da takwas a aikin jarida
Lagos – Prophet Itunu Onadeko, angon marigayiyar jarumar Nollywood, Temitope Osoba, ya yi zargin cewa jarumar ta rasu a wani ofishin ’yan sanda da ke Ikorodu a Jihar Legas.
Onadeko ya bayyana hakan ne yayin wata hira da Celestial Reality Check, sashen bincike na kafar yaɗa labarai ta cocin Celestial Church of Christ, a ranar Asabar.

Source: Instagram
Bayani kan mutuwar jarumar Nollywood
Zargin ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da ce-ce-ku-ce kan musabbabin mutuwar jarumar, inda wasu rahotanni da saƙonnin kafafen sada zumunta suka danganta rasuwarta da matsalolin da ta fuskanta sakamakon cutar kansar nono, in ji rahoton Punch.
Sai dai Onadeko ya musanta cewa ciwon kansar nono ne ya yi sanadin mutuwar Osoba, duk da cewa ya tabbatar da cewa ta taɓa fama da cutar tare da yin tiyata.
Onadeko, wanda shi ne jagora a cocin CCC Onibuore Cathedral da ke Bogije, yankin Ibeju-Lekki a Legas, ya ce wani mutum da ba ya iya tantance ko wanene ba ne ya kira shi da misalin ƙarfe 12 na dare domin sanar da shi mutuwar jarumar.
Ya ce:
“Wani mutum kawai ne ya kira ni da misalin ƙarfe 12 na dare ya ce ta rasu a wani ofishin ’yan sanda da ke Ikorodu.”
Sai dai faston ya ce bai san takamaiman ofishin ’yan sandan da Osoba ta rasu a cikinsa ba. Ya bayyana cewa bayan samun labarin, sai ya kai kansa wani ofishin ’yan sanda da ke kusa da shi.

Kara karanta wannan
Sojoji sun ragargaji 'yan ta'adda, an kashe fiye da 65 yayin da aka ceto mutane 360
Osoba ta je ganin wata mata
Onadeko ya ce Osoba ta dage sai ta je ganin wata mata mai suna Kehinde Osoba, wadda ya ce ita ma tana gudanar da coci, jim kaɗan kafin mutuwarta.
Ya ce jarumar ta kuma yi niyyar ganinsa, amma ya kasa zuwa saboda wasu shirye-shiryen coci da yake da su a lokacin.
“Ta dage sai ta ga Mrs Kehinde Osoba, ita ma tana da coci, duk da cewa ta ce tana son ganina ni ma. Da suka tafi wurin, na gaya musu cewa ba zan samu damar zuwa ba a ranar saboda shirye-shiryen coci.”
Onadeko ya ƙara da cewa wata mai gyaran gashi da Osoba ke kwana a gidanta ce ta raka ta zuwa wurin.
Ya ce sun ci gaba da sadarwa da ita, har ma ta wallafa wani saƙo mai cewa “Ogo tun tun” kafin daga bisani ya ji labarin mutuwarta.
An musanta wasu zarge-zarge
Prophet Onadeko ya kuma musanta wasu zarge-zarge da suka biyo bayan mutuwar Osoba, ciki har da ikirarin cewa an saka mata guba ko kuma an wulakanta ta kafin rasuwarta.

Kara karanta wannan
Fitattun 'yan TikTok 3 sun fara ganin sakamako bayan sun taɓa mutuncin shugaban ƙasa
Ya kuma ƙaryata zargin cewa ya samu damar mallakar kuɗaɗen da aka tara domin taimaka wa jarumar wajen biyan kuɗin tiyatar kansar nono, ko kuma ya yi amfani da kuɗin wajen gina cocinsa.

Source: Instagram
Osoba ta taɓa bayyana a bainar jama'a cewa ta yi fama da cutar kansar nono tare da samun magani da tiyata.
A shekarar 2024, jarumar ta sanar da komawarta cikin harkokin jama'a bayan shafe wani lokaci tana fama da matsalar, inda ta bayyana cewa wannan lokaci ya taimaka mata wajen samun waraka, ƙaruwa da ƙarfin gwiwa.
Sai dai sabuwar ikirarin da angonta ya yi ya ƙara jefa haske kan yanayin da ya dabaibaye mutuwar jarumar, yayin da har yanzu ba a samu cikakken bayani mai zaman kansa kan takamaiman musabbabin mutuwarta ba.
Kalli bidiyon tattaunawar a nan kasa:
Jarumar Nollywood ta mutu
A wani labari, mun ruwaito cewa, wata fitacciyar jarumar Nollywood da ke tashe, Omotola Odunsi ta riga mu gidan gaskiya.
Abokan aiki da jarumai a masana'antar shirya fina-finan da ke Kudancin Najeriya sun tabbatar da mutuwarta a sakonni daban-daban.
Sun bayyana alhini da jimaminsu bisa wannan rashi da suka yi tare da addu'ar Allah Ya ba iyalanta haƙuri da juriya.
Asali: Legit.ng
