
Albashin ma'aikata







Gwamnan jihar Nasarawa, abdullahi Sule ya ziyarci kasar China domin tattaunawa da kamfanin batir na Lithium a Nasarawa. Za a rika ba ma'aikata albashin N500,000.

Shugaban kungiyar kwadago na kasa, Kwamred Joe Ajaero ya bayyana cewa ba za su nade hannayensu, ana kallon gwamnati ta na kara wa 'yan kasa wahala ba.

Da safiyar yau Laraba 22 ga watan Janairun 2025, Gwamnan Benue, Hyacinth Alia, ya kai ziyarar bazata sakatariya inda ya gano yadda ma'aikata ke wasa da aikinsu.

Gwamnatin Abia ta amince da karin albashi ga sarakunan gargajiya, sake fasalin gudanarwarsu da kuma daukar matakan dakile tuki a hanyar da ba ta dace ba.

Karamar ministar kwadago, Nkeiruka Onyejeocha ta ce gwamnatin Tinubu za ta sake duba mafi ƙarancin albashin ma'aikata nan da ƙasa da shekaru biyu masu zuwa.

Gwamna Abba Yusuf ya saki N5bn ga masu fansho, ya kuma sanar da karin mafi karancin fansho zuwa N20,000. Abba ya ce Ganduje ya jefa 'yan fansho a cikin wahala.

Gwamnatin Kano ta jaddada aniyarta na tabbatar da biyan dukkanin 'yan fansho hakkokinsu kamar yadda ta yi alkawari kafin a zabe ta a shekarar 2023.

Tsofaffin ma'aikatan CBN da aka kora daga bakin aiki sun garzaya kotu su na kalubalantar yadda babban bankin ya saba doka wajen korarsu ba bisa ka'ida ba.

Malamai da ma'aikata karkashin JAC sun shiga yajin aiki a Bauchi, inda suka bukaci a aiwatar da tsarin albashi na CONPCASS da CONTEDISS. An rufe manyan makarantu.
Albashin ma'aikata
Samu kari