
Albashin ma'aikata







Malaman Ebonyi sun shiga yajin aikin sai baba-ta-gani bayan wasu shugabannin kananan hukumomi sun gaza biyan albashin watanni uku na malaman firamare.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya amince da yin kari a shekarun da likitoci da sauran ma'aikatan lafiya suke yi suna aiki. Za su samu karin shekara biyar.

Kamfanin KAEDCO ya yi martani ga kungiyar NUEE da ta shiga yajin aikin kan korar ma'aikata. Kamfanin ya tabbatar da cewa ma'aikata 450 kawai ya sallama daga aiki.

Shugaban hukumar kula da masu yi wa kasa hidima (NYSC), ya bayyana lokacin da za a fara biyan matasan da ke bautar kasa alawus na N77,00 duk wata.

Gwamnatin Tarayya ta fara sayar da shinkafa ga ma’aikata a Sokoto kan rangwamen ₦40,000, tare da tsarin “mutum daya, buhu daya” don hana taskancewa.

NYSC ta sanar da karin albashi ga mata masu yiwa kasa hidima daga N33,000 zuwa N77,000. Albashin zai fara aiki daga Fabrairun 2025, a cewar shugaban NYSC.

Gwamnatin jihar Sokoto ta yi magana kan lokacin fara biyan sabon mafi karancin albashi. Ta ce za ta fara biyan ma'aikatan sabon albashin daga watan Janairun 2025.

Gwamnatin jihar Oyo karkashin jagorancin Gwamna Seyi Makinde ta cika alkawarin da ta daukarwa ma'aikata inda ta fara biyan sabon mafi karancin albashi.

Gwamnan jihar Nasarawa, abdullahi Sule ya ziyarci kasar China domin tattaunawa da kamfanin batir na Lithium a Nasarawa. Za a rika ba ma'aikata albashin N500,000.
Albashin ma'aikata
Samu kari