Sakon da Bola Tinubu Ya Tura Wa 'Yan Dariƙar Tijjaniyya a Najeriya da Wasu Kasashe
- Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tura wakili wurin maulidin Sheikh Ahmad Al-Tijani, RTA, wanda ya gudana a jihar Kano
- A jawabin da ya tura, Tinubu ya bukaci shugabannin Tijjaniyya da mabiyansu na duniya su kauce tare da yakar tsattsauran ra'ayi
- Shugaban kasar ya ce bai kamata a yi amfani da addini wajen halatta kashe-kashen fararen hula ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kano, Nigeria - Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci shugabannin addini da su rika yin kakkausar magana kan ta’addanci, garkuwa da mutane da ayyukan ’yan bindiga.
Tinubu ya yi wannan kira ne ranar Lahadi a Kano, cikin sakon da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya isar a madadinsa yayin babban taron Mauludin Sheikh Ahmad Al-Tijani, RTA.

Source: Twitter
Sakon da ya isar ga yan Tijjaniyya a Kano
Vanguard ta ruwaito cewa Tinubu ya tura wannan sako ne ga Khalifan Darikar Tijjaniyya na duniya, malamai, shugabannin addini da mabiya daga Najeriya da sauran kasashe.
Shugaba Tinubu ya ce malaman addini na da muhimmiyar rawar da za su taka wajen dakile tashin hankali, tsattsauran ra’ayi da amfani da akida wajen tayar da rikici.
“Dole ne a rika jin muryoyinku a kai a kai kan kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, da ta’addanci, garkuwa da mutane, ’yan bindiga da amfani da addini wajen halatta zalunci,” in ji Tinubu.
Ya kuma bukaci kungiyoyin addini da hanyoyin sadarwarsu su kara karfafa wayar da kan jama’a kan zaman lafiya, ilimin addini, karatu da kuma tarbiyyar matasa masu nagarta.
"Ba a bautar Allah da kashe mutane"
Tinubu ya jaddada cewa ba za a iya cewa ana bautar Allah ta hanyar lalata rayukan mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, kamar yadda Tribune Nigeria ta ruwaito.
Ya ce:
“Sama da komai, iyayenmu malamai su ci gaba da koyar da cewa babu wata ibada ta gaskiya ga Allah da za ta ci gaba ta hanyar lalata rayuwar mutumin da Allah ya sanya ta zama mai tsarki.”

Kara karanta wannan
Tinubu ya aika saƙo cikin kaɗuwa da aka tabbatar da rasuwar babban malami a Najeriya
Ya kuma bayyana cewa taron na gudana ne a lokacin da duniya ke fuskantar rikice-rikice, rashin tabbas, sauyin yanayi, matsalar abinci da makamashi, ta’addanci da laifukan da suka ketare iyakokin kasashe.

Source: Facebook
Tinubu ya yaba wa Tijjaniyya
Shugaban ya ce Darikar Tijjaniyya, wadda ke da dimbin mabiya a Yammacin Afirka, Arewacin Afirka da sauran sassan duniya, na da muhimmiyar damar taimakawa wajen sasanta rikice-rikice da yaki da tsattsauran ra’ayi,
Ya ce gwamnati ta aminta da muhimmiyar rawar da malaman addini da sarakuna ke takawa wajen karfafa zaman lafiya a tsakanin al’umma, dakile yada labaran karya da kuma inganta zaman tare.
Shugabannin Tijjaniyya sun ziyarci Tinubu
A wani labarin, kun ji cewa Majalisar Koli ta Tijjaniyya ta duniya ta kai wa Shugaba Bola Tinubu ziyarar ta'aziyya kan rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi.
Tawagar daga Aljeriya, Najeriya da Senegal ta wakilci sama da mambobi miliyan 400 na darikar a duniya wajen mika sakon ta'aziyya ga Tinubu.
Asali: Legit.ng
