Ma'aikata Za Su Warwasa, Shugaba Tinubu Ya Shirya Cika Alkawarin da Ya Dauka

Ma'aikata Za Su Warwasa, Shugaba Tinubu Ya Shirya Cika Alkawarin da Ya Dauka

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

  • Gwamnatin Tarayya ta ce za ta fara biyan ragowar tallafin albashi da ta yi wa ma'aikata alkawari kafin tsakiyar watan Agusta
  • Ministan Kudi, Taiwo Oyedele ya ce gwamnatin tarayya tana cika alkawuran da ta dauka ga ma'aikata domin inganta walwalarsu
  • Kungiyar JPSNC ta bukaci gwamnati ta gaggauta warware sauran matsalolin da ma'aikata ke fuskanta a Najeriya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Gwamnatin Tarayya ta tabbatar wa ma'aikatan gwamnati cewa za ta fara biyan ragowar tallafin albashi (wage award) kafin tsakiyar watan Agusta, 2026.

Ministan Kudi kuma Mai Kula da Tattalin Arziki, Taiwo Oyedele nr ya bayyana hakan yayin wata ganawa da shugabannin kungiyar Joint Public Service Negotiating Council (JPSNC) karkashin jagorancin Kwamared Kabiru Ado Minjibir.

Ministan kudi.
Ministan kudi da harkokin tattalin arzikin Najeriya, Taiwo Oyedele a bakin aiki Hoto: Taiwo Oyedele
Source: Twitter

Daily Trust ta ce sanarwar da Ma'aikatar Kudi ta fitar ta ce ministan ya bayyana cewa gwamnati ta fara magance wasu daga cikin matsalolin da kungiyar ta gabatar tun kafin ta karbi takardarta a hukumance.

Kara karanta wannan

Babbar magana: Ma'aikata sun huro sabuwar wuta ga Shugaba Tinubu

Tinubu zai cika alkawarin tallafin albashi

A cewar ministan, ana kammala dukkan matakan da suka dace domin amincewa da biyan ragowar tallafin albashin, yana mai bayyana kwarin gwiwar cewa ma'aikatan da suka cancanta za su fara karbar kudaden kafin tsakiyar watan Agusta.

Ya ce:

"Idan gwamnati ta dauki alkawari, tana cika shi. Ba dabi'armu ba ce mu yi alkawarin da ba za mu iya cikawa ba. Idan akwai sauran batutuwa, za mu bayar da sahihin jadawalin lokaci sannan mu tabbatar da aiwatar da su."

Oyedele ya kuma bayyana cewa gwamnatin na bai wa batun karin girma muhimmanci, inda ake ci gaba da sarrafa sauran jerin sunayen ma'aikatan da suka rage bisa tsarin da aka amince da shi.

Ya umarci jami'an da abin ya shafa da su gaggauta duba takardun da kungiyar JPSNC ta gabatar tare da hada kai da ma'aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati domin hanzarta warware duk wasu matsalolin da suka shafi ma'aikata.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya yi magana da limaman Katolika suka cire tsoro, sun ja da Tinubu

Ministan ya amince cewa kungiyoyin kwadago sun nuna damuwa kan jinkirin aiwatar da wasu yarjejeniyoyi, amma ya tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da gina amincewa ta hanyar gaskiya, tattaunawa da kuma daukar matakan gaggawa.

Bola Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a fadar Aso Rock Hoto: Bayo Onanuga
Source: Twitter

Bukatun da ma'aikata suka mika

Tun da farko, shugaban kungiyar JPSNC ya bukaci gwamnati ta hanzarta warware matsalolin da suka hada da ragowar tallafin albashi, bashin karin girma, matsalar daidaiton albashi ga ma'aikatan lafiya da sauran batutuwan jin dadin ma'aikata.

Ya ce aiwatar da wadannan alkawura cikin lokaci zai kara tabbatar da zaman lafiya tsakanin gwamnati da ma'aikata tare da kara musu kwarin gwiwa.

Ma'sikata sun yi watsi da tayin N100,000

A wani labarin, kun ji cewa ana ci gaba da sukar tayin gwamnonin Najeriya na kara mafi karancin albashin ma'aikatan gwamnati daga N70,000 zuwa N100,000.

Kungiyar ma'aikatan gwamnatin tarayya (FWF) ta yi watsi da tayin gwamnonin, tana mai cewa adadin bai dace da halin da ma'aikata ke ciki ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262