Siyasar Najeriya
Shugaba Buhari ya yi alkawarin yi wa kowa adalci, wannan ya sa wani Gwamnan Kudu ya yabawa Buhari bayan ya kaddamar da wani aiki domin maganin cinyewar kasa.
Sabanin da ya ratsa PDP ya na iya sa Jam’iyyar adawa ta sake rasa kujerar Gwamna a 2020 inji Kungiyar PDP Youths for Justice wanda ta nemi a ja kunnen Dan Orhi.
Ba zan fito da Magajina da kai na ba, amma zan bari ayi zaben gaskiya inji Buhari. Shugaban ya kuma tabbatar cewa babu wanda zai yi amfani da kudi wajen samun kujera a 2023.
Wani tsohon bulaliyar majalisar dattawa, Roland Owie, a ranar Lahadi, 5 ga watan Janairu ya ce yankin Arewa za ta cigaba da rike mulki a 2023 don daidaito a lokacin da yankin kudu ta yi tana mulki tun 1999.
Mun ji cewa an hurowa karamin Ministan ilmi wuta a APC kan zargin hada-kai da PDP a zaben Imo. PDP dai ta ce a shirya ta ke ta karbe sa a jihar.
Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta yi kira ka shugaban kasa Muhammadu Buhari daya daina fita kasashen waje domin duba lafiyarsa kamar yadda ya yi kira ga yan Najeriya, domin ya kasance shugaba nagari abin koyi.
Wanda su ka yi takara da Buhari a 2011 a CPC ya ba shi shawara cewa ya tsaida mai kishi a 2023 ba Marasa gaskiya da kuma wadanda su ke da giyar mulki ba.
Watakila a binciki irinsu Rabiu Musa Kwankwaso da wasu ‘Yan riga-Malam-masallaci a PDP domin akwai kishin-kishin din cewa sun fara hangen 2023 tun a 2019.
Shugaban kwamitin yardaddu na jam'iyyar PDP, Sanata Walid Jibrin ya jawo hankulan jama'a ta yadda magoya bayan tsohon shugaban kasa Atiku Abubakar ke barazana ga rayuwarshi a kan tikitin takarar shugaban kasa na jam'iyyar a 2023..
Siyasar Najeriya
Samu kari