Siyasar Najeriya
Yarjejeniyar sirri da ake zargin an kulla tsakanin Tinubu da gwamnoni na PDP na ƙara rura rikicin shugabanci a jam'iyyar, yayin da Tinubu ke neman tazarce a 2027.
Tsohon dan majalisar wakilai, Tajudeen Yusuf, ya bukaci Atiku Abubakar ya hakura da yin takara a zaben 2027. Ya bukaci ya hakura tikitin PDP ya tafi yankin Kudu.
Tsohon mai ba shugaban kasa shawara, Hakeem Baba-Ahmed ya bukaci Bola Tinubu ya hakura da takara a 2027 domin ba matasa da sababbin jini damar shugabanci.
Tsofaffin ‘yan majalisar CPC na 2011, sun nada Al-Makura a matsayin jagora a APC, inda suka caccaki Nasir El-Rufa'i da tsohon Antoni Janar, Abubakar Malami.
Tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar PDP na kasa, Olabode George ya zargi Atiku Abubakar da Nyesom Wike da cin dunduniyar jam'iyyar. Ya bukaci su fice daga PDP.
Hukumar zabe ta INEC na son kawo sauyi a dokar zabe domin ba marasa katin PVC damar kada kuri'a a zaben 2027. Hakan zai rage kudin da INEC ke kashewa.
Timi Frank ya zargi Tinubu da tunzura Arewa da Kudu don burin dawowa mulki a 2027, ya ce ya na amfani da kabilanci da barazana don cimma manufarsa.
Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Dele Momodu, ya shawarci shugaban kasa Bola Tinubu da ka da ya yarda da 'yan siyasa masu sauya sheka zuwa APC.
Gwamnatin Akwa Ibom ta musanta rade-radin cewa Gwamna Umo Eno na shirin ficewa daga PDP zuwa APC a kasa bayan takwaransa na Delta, Sheriff Oborevwori ya gudu.
Siyasar Najeriya
Samu kari