Siyasar Arewa
Tsohon shugaban APC a Kwara, Bashir Bolarinwa, ya ayyana kudirinsa na tsayawa takarar gwamna, yana cewa yana da kwarewa da hangen nesa don magance matsalolin jiha.
Wannan rahoto ya duba yadda ƴaƴan tsofaffin shugabannin Najeriya da sarakuna ke shirin fafatawa a zaɓen 2027. An duba yadda ake ganin tasirin takararsu.
Bukola Saraki ya yi martani kan zargin fashin Offa, inda ya zargi Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq da shirya tugun siyasa a sanarwar yau 17 ga Afrilu, 2026.
Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jihar Legas ya kaddamar da sababbin jiragen kasa masu tarago 24 a jihar Legas. 'Yan Arewa na korafi kan cewa an bar su a baya.
Gwamna Abdullahi Sule ya ayyana Sanata Ahmed Wadada a matsayin wanda zai gaje shi a zaɓen 2027 domin ci gaba da mulkar jihar Nasarawa karkashin jam'iyyar APC.
A labarin nan, za a ji tsohon ɗan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana cewa yana da tarin masoya fiye da Rabi'u Musa kwankwaso da Aminu Waziri Tambuwal.
Shugaban gwamnonin Arewa kuma gwaman Gombe, Inuwa Yahaya ya ce rufin asirin mu na cikin zaben Bola Tinubu da sauran 'yan APC a zaben 2027 mai zuwa.
A labarin nan, za a ji yadda jigon adawa na jam'iyyar ADC, Injiniya Buba Galadima ya bayyana kwarin gwiwa a kan cewa za su yi nasara a kan Bola Tinubu a 2027.
Tsagin ADC a jihar Adamawa ya dakatar da Atiku Abubakar da Babachir Lawal daga jam'iyyar a yau Litinin, 13 ga Afrilu, 2026, kan zargin janyo rarrabuwar kai.
Siyasar Arewa
Samu kari