Masu Garkuwa Da Mutane
Gwamnatin jahar Katsina a karkashin jagorancin gwamna Aminu Bello Masari tare da hadin gwiwar rundunar Sojan kasa sun baiwa yan bindiga wa’adin sa’ao’i 48 su sako duk mutanen dake hannunsu ko kuma su fuskanci fushin hukuma.
Kaico! Allah Sarki, wasu miyagu yan bindiga sun sace tare da garkuwa da wasu malaman makarantar firamari guda biyu a kauyen Avbiosi na karamar hukumar Owan ta yamma a jahar Edo.
Rahotanni sun kawo cewa wasu jami’an hukumar kwastam na Najeriya su biyu da aka yi garkuwa dasu sun kubuta daga hannun masu garkuwan bayan kwanaki hudu da sace su.
Kwanan nan aka gano gidajen Marayu da su ka yi shekara da shekaru a boye. Kamar yadda mu ka samu labari daga bakin Fatima Abdullahi Dala ta na cewa gidan ya yi shekaru 25 a Jihar Kano babu lasisi.
Wani karamin yaro mai shekaru 14 ya mika kan sag a gungun miyagu yan bindiga da suka yi awon gaba da mahaifiyarsa a unguwar Juji, Sabon Tasha, cikin karamar hukumar Chikun ta jahar Kaduna.
Gungun yan bindiga sun kaddamar da hari a garin Beni dake cikin karamar hukumar Neja, inda suka yi awon gaba da babban limamin Masallacin Juma’an garin, Malam Umar Muhammad.
Wasu gungun miyagu yan bindiga sun tattara wasu jami’an hukumar kwastam guda biyu, tare da yin awon gaba dasu a wani shingen binciken ababen hawa dake Dan-Bedi cikin karamar hukumar Jibia ta jahar Katsina.
Dakarun rundunar Yansandan Najeriya sun ceto wani karamin yaro dan shekara 6, wanda Dan kwamishinan ruwa na jahar Bayelsa ne, Mista Nengi Talbot Tubonah, bayan kwashe makonni uku a hannun yan bindiga.
Rahotanni sun kawo cewa yan bindiga sun yi garkuwa da wani dan jam’iyyar All Progressives Congress (APC), James Ajulo a jihar Ondo. Ajulo ya kasance shugaban jam’iyyar mai mulki a Akungba-Akoko a karamar hukumar Akoko ta kudu maso
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari