Masu Garkuwa Da Mutane
Rahotanni sun kawo cewa jami’an tsaro da taimakon wani maharbi sun samo tarin makamai da alburusai wadanda ake zaton na yan fashi ne a dajin Lame-Burra, wani gagarumin maboyar miyagu a jahar Bauchi.
Wasu yan bindiga da ake zaton masu garkuwa da mutane ne sun sace yaron wani dan kasuwa a Suleja a Chaza, wani gari da ke wajen garin Suleja a jahar Niger.
Rundunar yan sanda a jahar Niger ta kama wata mata ‘yar shekara 32 wacce aka ambata da suna Hassana Bala kan yunkurin yin garkuwa da wani mutum dan shekara 23, Umar Sarkin Turaku na kauyen Kawo a karamar hukumar Kontagora.
Rundunar yan sandan jahar Katsina a yammacin ranar Litinin, 24 ga watan Fabrairu ta baje gawawwakin yan bindigar da ta kashe a yayin wani arangama a Maraba Kankara da ke karamar hukumar Kankara na jahar.
Rahotanni sun kawo cewa fusatattun matasa a garin Otuo da ke karamar hukumar Owan na jahar Edo sun babbaka wasu mutane hudu a ranar Litinin, 24 ga watan Fabrairu.
Rundunar Yansandan jahar Nassarawa ta sanar da kama wata mata yar shekara 29 mai suna Paulina Santos wanda ta hada baki da wasu miyagun mutane suka yi garkuwa da mahaifiyar kawarta.
Jami’an rundunar Yansandan Najeriya reshen jahar Kaduna sun samu nasarar kama wasu miyagun masu garkuwa da mutane guda uku da suka dade suna fitinar jama’an jahar Kaduna, tare ceto wata budurwa daga hannunsu.
Al’ummar garin Uratta na karamar hukumar Owerri ta Arewa na jahar Imo sun rushe gidaje guda uku mallakin wani kasurgumin mai garkuwa da mutane, Okechukwu Uche biyo bayan mutuwar matar babban basaraken garin, Uwargida Ugoeze Comfor
Rahotanni sun kawo cewa wasu yan bindiga da ba a sani ba sun yi garkuwa da jami’an hukumar NSCDC a ranar Alhamis, 20 ga watan Fabrairu a yankin Ajegwu, karamar hukumar Ofu.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari