Dalilin da Ya Sa Bala Adamu Ya Amince Ya Zama Dan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa a 2027

Dalilin da Ya Sa Bala Adamu Ya Amince Ya Zama Dan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa a 2027

  • Bala Adamu Ibrahim ya ce ya amince da zama abokin takarar Gwamna Seyi Makinde na jam'iyyar APM saboda ya yarda da kwarewarsa
  • 'Dan takarar mataimakin shugaban kasar ya bayyana zaben da aka masa a matsayin babban abin alfahari ga Bauchi, Darazo da yankin Sade
  • Bala Adamu tsohon ma'aikacin gwamnati ne kuma gogaggen dan siyasa da dan kasuwa, ya taba rike mukaman SSA a gwamnatin Isa Yuguda

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Bauchi, Nigeria - Ɗan takarar mataimakin shugaban kasa na jam'iyyar APM, Bala Adamu Ibrahim ya bayyana dalilin da ya sa ya amince ya zama abokin takarar Gwamna Seyi Makinde.

Gwamna Makinde na jihar Oyo shi ne dan takarar shugaban kasa na APM a zaben 2027, yayin da daga bisani aka dauko Bala Adamu a matsayin mataimakinsa.

Kara karanta wannan

Peter Obi ya bayyana yiwuwar haƙura da neman takarar shugaban kasa, ya kawo dalili

Makinde.
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar APC, Gwamna Seyi Makinde ya karbi tutar jam'iyya Hoto: Seyi Makinde
Source: Facebook

Daily Trust ta ce da yake tsokaci kan haka, Bala Adamu ya bayyana cewa ya amince da zama dan takarar mataimakin shugaban kasa ne saboda yana da cikakken yakini cewa Makinde na da kwarewar da za ta ciyar da Najeriya gaba.

Ya ce Bauchi ta samu babban matsayi

A wata tattaunawa ta wayar tarho, Ibrahim ya ce Makinde ba kawai abokinsa ba ne, har ila yau babban abokin tafiyarsa ne a siyasa.

A cewarsa:

"Ina alfahari matuka da wannan nadin da aka yi min a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa na APM. Wannan ba kawai girma ne a gare ni ba, har ma wani tarihi ne ga al'ummata da kuma jihar Bauchi."

Bala ya ce tikitin APM ya zama abin alfahari ga jihar Bauchi, karamar hukumar Darazo da kuma al'ummar Sade, domin shi ne karo na farko da dan yankin ya samu irin wannan babban matsayi a siyasar Najeriya.

Kara karanta wannan

Tafiyar Pantami ta samu gagarumar nakasu, tsohon sanata ya yi murabus daga PDP

Wanene Bala Adamu Ibrahim?

Bincike ya nuna cewa Bala Adamu Ibrahim, wanda aka fi sani da Bala Sade, dan siyasa ne kuma dan kasuwa mai shekaru 51. Dan asalin gundumar Sade ce da ke karamar hukumar Darazo a jihar Bauchi.

Shi dan wani tsohon ma'aikacin karamar hukuma ne wanda ya yi aiki a matsayin mai kula da harkokin gandun daji.

Tafiyar Bala Sade a siyasa

Rahotanni sun nuna cewa Bala ya fara aiki a gwamnati tun kafin fara Jamhuriya ta Hudu a shekarar 1999 daga bisani ya yi ritaya.

Bayan haka ya tsunduma siyasa, inda ya nemi kujerar majalisar dokokin jihar Bauchi sau biyu tsakanin 1999 da 2003 karkashin jam'iyyar PDP a karamar hukumar Darazo.

A zamanin gwamnatin tsohon gwamna Isa Yuguda, an nada shi Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Matasa (SSA), Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Zabe a Hukumar Zaben Bauchi (BOSIEC).

Gwamna Seyi Makinde.
Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde a fadar gwamnatinsa da ke Ibadan Hoto: Seyi Makinde
Source: Facebook

Dangantakarsa da Gwamna Makinde

Wata majiya ta kusa da Bala Sade ta bayyana cewa yana da kusanci sosai da Seyi Makinde, har ma ya taba zama daya daga cikin masu taimaka masa.

Kara karanta wannan

Fadar shugaban kasa da Gwamna Makinde sun samu sabani kan ceto dalibai a Oyo

Majiyar ta ce a wannan lokaci ne dangantakarsu ta kara karfi, lamarin da ya sa Ibrahim ya shafe lokaci mai tsawo yana zaune a Ibadan.

APM ta hango nasarar Makinde

Kun ji cewa APM ta bayyana kwarin gwiwar cewa ɗan takararta na shugaban ƙasa, gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, zai yi nasara a zaɓen 2027.

Jam'iyyar ta ce tana ganin Makinde ya samu karɓuwa a wurin 'yan Najeriya a matsayin wanda zai gaji shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.

APM ta tabbatar da cewa ta tura sunayen Makinde da sauran 'yan takararta zuwa shafin INEC bayan karbar lambobin shigar da bayanai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262