Manyan Labarai A Yau
Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara, ya shawarci kwamishinan 'yan sandan jihar da sauran jami'an rundunar da su guji sanya siyasa a cikin aikinsu.
Kungiyar NUF ta yi kira ga jam'iyyar PDP da ta hukunta ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike. Kungiyar ta ce kalaman Wike rashin ɗa'a.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na ci gaba da ziyarar aiki a kasar China. Shugaba Tinubu ya shiga wata ganawa da shugaban kasar China, Xi Jinping.
Aliko Dangote ya yi jawabi yayin da matatar Dangote ta fara fitar da man fetur da aka tace a Najeriya. Ya ce man fetur zai wadata a gidajen man Najeriya.
Hajiƴa Dada Yar'adua, mahaifiyar tsohon shugaban ƙasa, Marigayi Umaru Musa Yat Adua ta kwanta dama bayan fama da jinya a asibitin koyarwa da ke jihar Katsina.
Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya fara daukar matakai kan gobarar da ta tashi a gidan gwamnatin jihar. Gwamnan ya kafa kwamitin bincike.
Babbar kotun tarayya da ke Abuja wacce ta fara sauraron shari'ar masu zanga zangar da aka gurfanar a gabanta ta tura su zuwa gidan gyaran hali a Abuja da Suleja.
Miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun tafka ta'asa a jihar Sokoto. 'Yan bindigan sun hallaka jami'in dan sanda da wani dan banga a wani hari da suka kai.
Matatar mai ta Dangote ta shirya fara sayar da man fetur a kasuwa. Matatar da gwamnati na tsara yadda za a rika jigila tare da sayar da man fetur din a kasuwa.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari