'Mutumin da Za a Dorawa Alhaki idan Wani Abu Ya Samu El Rufai'

'Mutumin da Za a Dorawa Alhaki idan Wani Abu Ya Samu El Rufai'

Kakakin jam'iyyar ADC, Bolaji Abdullahi, ya ce gwamnatin APC na tsare Nasir El-Rufai saboda siyasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ya yi zargin ana hana tsohon gwamnan Kaduna shiga zaɓen 2027 domin raunana jam'iyyar ADC mai adawa

Bolaji Abdullahi ya ce idan wani abu ya samu El-Rufai, za a ɗora alhakin hakan kan Shugaba Bola Tinubu

FCT, Abuja – Sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam'iyyar ADC, Bolaji Abdullahi, ya yi magana kan ci gaba da tsare Malam Nasir Ahmad El-Rufai.

Bolaji Abdullahi ya ce za a ɗora alhakin duk wani abu da ya samu tsohon gwamnan na jihar Kaduna, kan Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

An yi magana kan tsare El-Rufai
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai Hoto: Bello El-Rufai
Source: Facebook

Kakakin na jam'iyyar ADC ya bayyana hakan ne yayin da yake magana a wata hira da tashar Symfoni tv.

An yi zarge-zarge kan tsare El-Rufai

Bolaji Abdullahi ya ce ci gaba da tsare El-Rufai ba shi da alaƙa da doka ko hukuncin laifi, illa siyasa kawai.

Kara karanta wannan

An goyi bayan harbe 'yan ta'adda da zarar an gan su ba tare da jiran izini ba

Tsohon ministan ya kuma yi zargin cewa ana ci gaba da tsare El-Rufai ne domin hana shi shiga zaɓen shekarar 2027, da nufin raunana jam'iyyar ADC.

"To, ba mu san abin da ya faru ba, amma abin da yake a bayyane shi ne wannan ba batun doka ba ne, ba batun laifi da hukunci ba ne, siyasa ce."
"A yau ba a tsare Malam Nasir El-Rufai saboda ya aikata wani laifi ba, domin idan haka ne, kotu ce za ta yanke hukunci ta ce yana da laifi ko ba shi da laifi."
"Amma ci gaba da tsare shi ba tare da iyaka ba yana nuna akwai wata manufa. Shi ya sa muka yi imanin cewa gwamnatin APC na son ci gaba da tsare Malam Nasir El-Rufai domin tabbatar da cewa bai shiga wannan zaɓe ba, kuma bai ƙarfafa adawa ba. Wannan ne ainihin shirinsu."

- Bolaji Abdullahi

Ya ce El-Rufai ya taimaki Tinubu

Bolaji Abdullahi ya kuma ce El-Rufai ya taka muhimmiyar rawa wajen haɗa kan Arewacin Najeriya domin marawa Bola Tinubu baya a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2023.

Kara karanta wannan

Kai mutane Hajji, taimakon almajirai da ayyukan Peter Obi a Arewa

"Lokacin da wasu a Arewa suke cewa dole sai ɗan Arewa ya tsaya takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023, Malam Nasir El-Rufai ne ya jagoranci haɗa kan Arewa domin goyon bayan Shugaba Bola Tinubu tare da wasu mutane."
"Na kuma ga bidiyo inda Shugaba Bola Tinubu da kansa yake roƙon Malam Nasir El-Rufai kada ya bar ƙasar nan, domin gwamnati za ta buƙace shi."

- Bolaji Abdullahi

An nemi a saki El-Rufai
Malam Nasir Ahmad El-Rufai, tsohon gwamnan jihar Kaduna Hoto: @elrufai
Source: Twitter

"Tinubu zai ɗauki alhaki"

Abdullahi ya kuma yi iƙirarin cewa lafiyar El-Rufai na ci gaba da tabarbarewa.

"Zan sake maimaita wannan a nan. Allah Ya kiyaye, idan wani abu ya samu Malam Nasir El-Rufai, Shugaba Bola Tinubu ya sani cewa, ko da ba da nufinsa aka kai ga hakan ba, za a ɗora alhakin hakan a kansa, kuma sakamakon abin ba zai kasance mai sauƙin hasashe ba."
"Ko dai ya saki Malam El-Rufai beli ya bar shi ya fuskanci shari'a, ko kuma ya ci gaba da tsare shi har zuwa ƙarshen wa'adin mulkinsa."
"Idan muka karɓi mulki, za mu binciki abin da ya faru, sannan a ɗora wa kowa alhakin da ya dace da shi."

- Bolaji Abdullahi

Kara karanta wannan

"Ina da hujja": Al Mustapha ya yi magana kan batun rasuwar Janar Abacha

An kai karar likitan El-Rufai

A wani labarin kuma, kun ji cewa Hukumar ICPCta shigar da ƙarar likitan Nasir El-Rufai gaban Hukumar Kula da Ayyukan Likitoci da Masu Haƙora ta Najeriya (MDCN).

ICPC ta nemi a hukunta Farfesa Bello Abubakar bisa zargin ƙirƙirar rahoton lafiya da aka yi amfani da shi wajen neman belin tsohon gwamnan na jihar Kaduna.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng