Manyan Labarai A Yau
Wani jirgin kwale kwale mai dauke da fasinjoji a jihar Bauchi ya kife a cikin tsakiyar kogi. An samu nasarar ceto mutum bakwai yayin da aka nemi sauran aka rasa.
Gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Duoye Diri, ya nuna kwarin gwiwarsa kan cewa nan ba ɗa jimawa ba za a shawo kan rikicin jam'iygar PDP. Ya ce suna kokari hakan.
Ambaliyar ruwa ta shafi mutane masu yawa a jihar Zamfara. Sama da mutum 10,000 ne suka rasa matsugunansu. Gwamnan jihar ya yi jajen aukuwar hakan.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya isa kasar China domin gudanar da ziyarar aiki a kasar. Tinubu zai gana da shugaban China da sauran manyan 'yan kasuwa.
Dandalin sada zumunta na X ya daina aiki a cikin kasar Brazil mai mutane miliyan 200, sakamakon kazamin fada tsakanin Elon Musk da wani alkali dan kasar.
Karamin ministan tsaro, Mohammed Bello Matawalle, ya sha alwashin kawo karshen 'yan bindigan da suka addabi yankin Arewa maso Yammaci na Najeriya.
Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya bukaci masu siyasantar da matsalar rashin tsaro a jihar da su daina. Ya ce ko kadan ba za su lamunci hakan ba.
Mutanen gari a ƙauyen Matusgi da ke ƙaramar hukumar Talata Mafara a jihar Zamfara sun yi fito na fito da 'yan bindiga. Sun hallaka mutum 37 har lahira.
Yankin Arewacin Najeriya na da al'adar samar da fitattun 'yan wasan kwallon kafa. Yankin ya samar da 'yan wasan da suka zama fitattu a gida da wajen Najeriya.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari