"Sojoji Kadai ba Za Su Iya ba"; Sarkin Potiskum Ya Fadi Hanyar Magance Matsalar Tsaro a Najeriya
- Mai martaba Sarkin Potiskum ya ce ba za a kawo ƙarshen matsalar tsaro da amfani da ƙarfin soja kaɗai ba
- Babban basaraken ya buƙaci gwamnati ta magance talauci, rashin adalci da sauran matsalolin zamantakewa da ke haddasa rikice-rikice
- Ya jaddada cewa sarakunan gargajiya na da muhimmiyar rawa wajen samar da zaman lafiya da warware rikice-rikicen al'umma
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Potiskum, Yobe - Mai Martaba Sarkin Potiskum, Alhaji Umaru Bubaram Ibn Wuriwa Bauya, ya bukaci shugabannin Najeriya su rungumi hanyoyin da suka fi haɗa kan jama'a wajen magance matsalar tsaro.
Sarkin ya ce amfani da ƙarfin soja kaɗai ba zai iya kawo ƙarshen matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta ba.

Source: Facebook
Jaridar The Punch ta ce Sarkin Potiskum ya bayyana cewa bambance-bambancen da ke akwai a Najeriya na daga cikin manyan ƙarfinta yayin da yake magana kan halin da kasa take ciki.
Ya kuma bukaci gwamnatoci a matakai daban-daban su magance talauci, rashin adalci da sauran matsalolin tattalin arziki da zamantakewa da ke haddasa rikice-rikice a faɗin ƙasar.
Ya bayyana makamin da Najeriya ke da shi
"Najeriya ƙasa ce mai sarkakiya amma cike da kyawawan bambance-bambance, tana da ƙabilu sama da 300, kowacce da al'adunta da harshenta."
"Bai kamata a ɗauki bambance-bambance a matsayin rauni ba. Su ne babban ƙarfinmu. Ya dace kowane ɗan Najeriya ya ji cewa yana da gurbi a ƙasarsa, domin hakan yana ƙarfafa haɗin kan jama'a wajen ci gaban ƙasa." In ji shi
Ya yi magana kan matsalar tsaro
Game da matsalolin tsaro da ake fama da su a ƙasar, Sarkin ya ce dole ne gwamnati ta wuce amfani da ƙarfi idan tana son samar da zaman lafiya mai ɗorewa.
"Ba za a magance matsalar tsaro da amfani da ƙarfi kaɗai ba. Dole ne shugabanni su magance tushen matsalolin tattalin arziki da zamantakewa da ke haddasa rikice-rikice cikin gaskiya da adalci." In ji shi
Ya ƙara da cewa shugabannin ƙasa su riƙa kallon kansu a matsayin iyaye ga dukkan 'yan ƙasa ba tare da la'akari da bambancin ƙabila, addini ko ra'ayin siyasa ba.
"Shugaban ƙasa nagari ya kamata ya zama kamar uba nagari, yana sauraron kowane ɗansa ba tare da nuna wariya ba, yana gyara kuskure cikin hikima tare da tabbatar da cewa kowa yana jin ana daraja shi. Idan shugabanni suka fifita jin daɗin al'umma a kan muradunsu na kashin kansu, ƙasa za ta samu ci gaba mai ma'ana."
Rawar sarakunan gargajiya wajen zaman lafiya
Sarkin Potiskum ya kuma jaddada muhimmancin sarakunan gargajiya wajen inganta zaman lafiya da hana rikice-rikicen al'umma.
"Saboda muna rayuwa tare da jama'a, mun fi sanin matsalolinsu kai tsaye. Wannan yana ba mu damar ba gwamnati shawara, sauƙaƙa tattaunawa cikin lumana da kuma warware matsalolin cikin gida kafin su ta'azzara."
"Ya kamata sarakunan gargajiya su jagoranci ci gaban al'umma, su bunƙasa ilimi, su tallafa wa harkokin tattalin arziki tare da inganta zaman lafiya." In ji shi.
A ƙarshe, Ibn Wuriwa Bauya ya bukaci shugabannin siyasa da na gargajiya su gudanar da mulki cikin adalci, riƙon amana da gaskiya.

Source: Original
'Yan bindiga sun hallaka mutane a Sokoto
A wani labarin kuma, kun ji cewa 'yan bindiga sun kai wani harin ta'addanci a jihar Sokoto inda suka kashe mutane.
Akalla mutane hudu ne suka rasa rayukansu yayin da wasu suka jikkata a harin da 'yan bindigan suka kai a karamar hukumar Sabon Birni.
Asali: Legit.ng

