Manyan Labarai A Yau
Kotu ta yanke wa Babagana Habeeb shekaru 10 a gidan yari kan sayar wa Boko Haram man fetur, bayan an shafe shekaru 10 ana shari'a. Alkali ya yi hukunci na ban mamaki
CBN ya fitar da sababbin dokokin BVN da za su fara aiki daga ranar 1 ga Mayu, 2026. Legit Hausa ta tataro abubuwa 5 da ya kamata ku sani gabanin wa'adin.
Shugaban majalisar dokokin Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya gindaya sharuddan fara tattaunawa da Amurka. Ya ce dole sai an cika su kafin a fara tattaunawa.
Tsohon shugaban jam'iyyar APC a jihar Jigawa, Ado Kiri, ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar. Ya nuna godiyarsa kan damar da aka ba shi ta kasancewa a jam'iyyar.
Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa kasarsa ba za ta zuba ido tana kallon Spain tana sukar manufofinta ba, za ta maida martani.
Gwamnatin jihar Bauchi ta tashi tsaye don dakile matsalar ayyukan 'yan bindiga. Gwamnatin ta rufe wasu kasuwanni da ake sayar da shanu a kananan hukumomi hudu.
'Yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a jihar Plateau. Tsagerun 'yan bindiga sun kashe mutanen da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba.
Ministan tsaron Pakistan, Khawaja Asif ya bayyana cewa Isra'ila ce babbar matsala a duniyar yau, ta zama karfen kafa ga al'ummar duniya wajen zubar da jini.
Shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual, Primate Elijah, ya yi hasashe kan tazarcen shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, a zaben shekarar 2027 mai zuwa.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari