Shin da Gaske Ma'aikatar Kudi Ta Bukaci Sababbin Ma'aikata Su Biya N50,000?

Shin da Gaske Ma'aikatar Kudi Ta Bukaci Sababbin Ma'aikata Su Biya N50,000?

  • Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya ta yi martani kan saƙon da ke neman sababbin ma’aikata su biya N50,000
  • A cikin wata sanarwa, ma’aikatar ta bayyana cewa ba a biyan kuɗin gudanarwa ko na fara aiki a tsarin ɗaukar ma’aikata
  • Hakazalika, ma'aikatar kudin ta shawarci jama’a su guji biyan kuɗi ko bayyana bayanansu ga masu wannan salo na damfara

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya ta nesanta kanta da wani saƙon damfara da ake yaɗawa sababbin ma’aikatan da aka ɗauka aiki, wanda ke umartarsu su biya N50,000 a matsayin kuɗin gudanarwa kafin su fara aiki.

Shugabar Sashen Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na ma’aikatar, Efe Ovuakporie, ta bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Laraba, 29 ha watan Yulin 2026.

Batun cewa a biya kudi a ma'aikatar kudi
Ministan kudi, Taiwo Oyedele Hoto: @taiwooydele
Source: Facebook

Jaridar Tribune ta ce Efe Ovuakporie tace masu damfara ne suka ƙirƙiri saƙon domin yaudarar masu neman aiki ta hanyar amfani da sunan Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya.

Kara karanta wannan

Yaki da yunwa: Oluremi ta fadi yadda Tinubu ya tallafa wa yan kasa da abinci

Abin da saƙon bogin ya ƙunsa

A cewar sanarwar, saƙon ya yi iƙirarin ƙarya cewa Sashen Gudanar da Harkokin Ma’aikata ya umarci sababbin ma’aikata su biya kuɗin gudanarwa kafin su fara aiki.

Sai dai ma’aikatar ta bayyana cewa ba ta bayar da irin wannan umarni ba, yayin da ta kuma jaddada cewa saƙon bai fito daga wani ofishi ko jami’in Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya ba.

Tsarin ɗaukar ma’aikatan gwamnati

Ma’aikatar ta ce ana ɗaukar ma’aikata a Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya ne bisa tsare-tsare da ƙa’idojin Hukumar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya.

“Babu wani mataki a tsarin ɗaukar ma’aikata, tattara takardu ko shigar da sababbin ma’aikata aiki da ake buƙatar masu neman aiki ko waɗanda aka ɗauka su biya kuɗin gudanarwa, sarrafa takardu ko na fara aiki.” In ji ta

Saboda haka, ma’aikatar ta shawarci masu neman aiki da sauran jama’a su yi watsi da saƙon damfarar, jaridar The Punch ta kawo labarin.

Kara karanta wannan

An daura auren gata ga mutum 300 a Kebbi, gwamnati za ta cigaba da shirin

Haka kuma, ta gargaɗe su da kada su biya wani kuɗi ko su bayyana bayanansu na sirri da na kuɗi ga mutanen da ke bayan wannan damfara.

An nemi a kai rahoton masu damfara

Ma’aikatar ta buƙaci duk wanda ya samu irin wannan saƙo ko yake da bayanan da za su taimaka wajen gano waɗanda ke da hannu a damfarar ya kai rahoto ga hukumomin tsaro da suka dace.

Ta ce ana iya sanar da ma’aikatar ta hanyoyin sadarwarta na hukuma domin taimakawa wajen gano masu aikata laifin.

Ma'aikatar kudi ta musanta neman kudi a hannun ma'aikata
Ministan kudi Taiwo Oyedele tare da takwaransa na sufurin jiragen sama, Festus Keyamo Hoto: @taiwooyedele
Source: Twitter

Sanarwar ta ce Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya za ta ci gaba da tabbatar da gaskiya, adalci da riƙon amana a dukkan matakan ɗaukar ma’aikata.

Ta ƙara da cewa za ta ci gaba da haɗa kai da hukumomin da suka dace domin kare jama’a daga ayyukan damfara da ake yi da sunanta.

Tinubu ya amince da aikin N46bn a MAKIA

A wani labarin kuma, kun ji cewa Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ware Naira biliyan 46 domin gyara tashar jirgin sama ta Malam Aminu Kano (MAKIA).

Shugaba Tinubu ya amince da kudaden ne domin sake shimfiɗa da kuma sake gina titin saukar jiragen sama na biyu a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng