"Za Mu Auri Kyawawan"; 'Yan Bindiga Sun Yi Sabuwar Barazana kan Mutane 176 da Suka Sace
- Yan uwan aƙalla mutane 176 da ’yan ta’adda suka sace a ƙaramar hukumar Kaiama ta jihar Kwara sun sake roƙon gwamnati ta gaggauta kuɓutar da su
- ’Yan uwansu sun ce sun tara sama da Naira miliyan 155 domin biyan kuɗin fansa, amma ana zargin masu garkuwar sun ƙi karɓar kuɗin
- An ce ’yan ta’addan sun yi barazanar aurar da matan da suke ganin kyawawa ne tare da kashe sauran waɗanda suke riƙe da su
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Kwara - 'Yan uwan aƙalla mutane 176 da ’yan ta’adda suka sace a ƙaramar hukumar Kaiama ta jihar Kwara sun sake roƙon gwamnatin tarayya da ta jihar da su gaggauta kuɓutar da ’yan uwansu bayan kusan watanni shida suna hannun masu garkuwa.
Wannan na zuwa ne yayin da ake zargin masu garkuwar sun yi barazanar aurar da matan da suke ganin suna da kyau tare da kashe sauran mutanen da suke riƙe da su.

Kara karanta wannan
Saudiyya ta shiga tsaka mai wuya, Iran ta matsa mata lamba ta fannoni 3 a yaki da Amurka

Source: Original
Barazanar da ’yan ta’adda suka yi
Da yake magana a wata hira da BBC Hausa ta yi, Abdul Ibrahim, ɗan asalin Kaiama, ya ce ’yan ta’addan sun yi barazanar tilasta wa matan da suke ganin suna da kyau auren dole.
Ya ƙara da cewa masu garkuwar sun yi barazanar kashe sauran waɗanda suke riƙe da su idan ba a biya musu buƙatunsu ba.
Ibrahim ya roƙi gwamnatin jihar Kwara da gwamnatin tarayya da kuma hukumomin tsaro su ƙara ƙaimi wajen ceto mutanen.
Ya ce iyalan waɗanda aka sace sun yi amfani da kusan duk wata hanya da suke da ita domin kuɓutar da su, amma abin bai yi nasara ba.
A cewarsa, al’ummomin da lamarin ya shafa sun haɗa kai tare da tara sama da Naira miliyan 155 domin biyan kuɗin fansa.
Sai dai ya ce ana zargin ’yan ta’addan sun ƙi karɓar kuɗin duk da ƙoƙarin da aka yi na amfani da su wajen samun ’yancin mutanen.
Zanga-zangar Kaiama ba ta yi tasiri ba
Ibrahim ya ƙara da cewa zanga-zangar lumana da al’ummar Kaiama suka shirya ma ba ta jawo irin matakin da suke fata daga hukumomi ba.
Shi ma da yake magana, Dan Sardaukin Kaiama, Suleiman Bukata, ya roƙi gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro su yi irin ƙoƙarin da ya kai ga ceto waɗanda aka sace a jihar Oyo.
Ya ce ya kamata a faɗaɗa irin wannan aiki zuwa Kaiama, inda daruruwan mazauna yankin suka shafe watanni suna cikin sansanonin ’yan ta’adda.
Bukata ya ce nasarar kuɓutar da waɗanda aka sace a Oyo ta sake raya fata a zukatan iyalan mutanen Kaiama.

Source: Facebook
A cewarsa, al’ummar Kaiama sun cancanci samun irin jajircewa da kariyar da hukumomi suka bayar wajen ceto waɗanda aka sace a Oyo.
Ya jaddada cewa kowace rana da mutanen ke ci gaba da zama a hannun masu garkuwa na ƙara jefa su cikin haɗari da wahalhalun da ba a iya misaltawa.
'Yan bindiga sun hallaka Kanal na soja
A wani labarin kuma, kun ji cewa hatsabiban 'yan bindiga dauke da makamai sun kashe Kanal Abdussalam Ude, wani jami’i mai aiki a rundunar sojojin Najeriya a Abuja.
Miyagun 'yan bindigan sun kuma harbi matarsa a gidansu da ke yankin Kurudu na babban birnin tarayya, Abuja.
Asali: Legit.ng

